Matasa Da Rayuwa



Dan'Adam yana da hakkin rayuwa, kamar yadda kuma rayuwar hakkinsa ce, haka nan ma samar masa da abubuwan da rayuwar take bukatuwa da su....sannan kuma yana daga cikin hakkinsa a bude masa hanyoyin ayyuka da kuma 'yancin samun abin hannu da kuma mallaka....kuma hakkinsa ne ya samu nasa rabon na albarkatun kasar da yake raye cikinta....

Muna iya ganin hakkokin dan'Adam a fili cikin fadin Allah Madaukakin Sarki:

"Kuma kasa ya aza ta domin talikai". (Surar Rahman, 55: 10)

Don haka an sanya kasa ne don kowa da kowa ya amfana da ita, kuma ba ya halalta ga wani mutum ya ajiye ta a matsayin kayansa kawai hana saura amfanuwa da ita.....

Dan'Adam wani sashi ne na wannan al'umma, yana da hakkin amfanuwa da dukkan abubuwan da suke cikin al'ummarsa....

Hakika kange amfani da alherorin da suke cikin kasa ga wata al'umma ko kuma kungiya da kuma haramta wa wata, zalunci ne da kuma gaba da dokokin rayuwa da kuma ka'idojin adalci.... Alkur'ani mai girma yana tabbatar da wannan ka'ida cikin fadinSa Madaukakin Sarki:

"Lalle Allah Na yin umurni da adalci da kyautatawa....". (Surar Nahl, 16: 90)

Don haka "mutane daidai suke kamar hakwaran matsefin kai", kamar yadda Manzon Allah (s.a.w.a.) ya fadi.

Lalle babu makawa a duk lokacin da mutane suka yi shiru kan zalunci da kuma babakeren da ake musu, to cutarwar za ta koma ga kowa da kowa ne, daga karshe sai ya zamanto wata kungiya ta azzalumai ta hau kan dukkan al'umma da kuma raunana ta.

Don haka, kamar kowane mutum yake kokari wajen sama wa kansa 'yanci, haka nan ya za ma wajibi a kansa ya yi kokari wajen samar wa sauran mutane ma, kada ya takaita shi ga kansa kawai.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 next