Ajali KoWa'adi



Sa'annan a bisa wanna doka ta ajali wacce ta mamaye komai kuma babu wani abu da ya isa ya fita daga wannan doka ta Allah mai gama-gari, kamar yadda daidaikun mutane suke da ajali haka nan ma al'umma take da ajali, muna iya ganin fadin madaukaki a kan wanna lamari: “Kuma kowace al’umma tana da ajali, idan ajalinsu ya zo ba sa jinkirin awa daya, kuma ba sa gabata. gaggauta musu”[9]. Da fadinsa mai girma; “Ba ma halakar da alkarya sai tana da lokaci kayyadajje. Babu wata al’umma da take rigon ajalinta kuma ba ta jinkiri[10].

Amma kamar yadda ya gabata dukkan al'umma da kuma daidaikun mutane suna da ajali iri biyu ne, akwai ratayayyen ajali wanda yana nufin koda yaushe mutuwa da ajali suna iya riskar halittu, amma wadannan ajaloli ne da ana iya ketare su a wuce su da kiyayewa da sadaka da sadar da zumunci da ayyukan alheri, da sadaka[11], wadannan abubuwa ne da suke fadada nisan ajaloli. A irin wannan lamarin ne Imam Sadik (a.s) yake cewa: Mutane suna rayuwa da kyawawan ayyukansu fiye da yadda suke rayuwa da shekarunsu, kuma suna mutuwa da zunubansu fiye da yadda suke mutuwa da ajalolinsu[12].

Kuma a nan muna iya ganin yadda kur'ani mai daraja ya yi nuni da wannan a fadin madaukaki (s.w.t) “Shi ne wanda ya halicce ku da tabo sannan sai ya kaddara muku ajali kuma da akwai wani ajalin ambatacce gunsa…[13]. Don haka ne a game da tafsirin wannan ayar sai muka ga abin da gidan annabta daya daga alayen Annabi Muhammad (s.a.w) ya karfafa a kan haka yana mai cewa: Ajalin nan da ba ambatacce ba dakatacce ne, yana gabatar da wanda ya so daga gareshi kuma ya jirkinta wanda ya so daga gareshi, amma ajali ambatacce shi ne wannan da yake saukar da abin da yake so ya kasance daga dare mai daraja (Lailatul kadr) zuwa irin wannan dare shekara mai zuwa, kuma wannan shi ne fadin Allah madaukaki: “… Idan ajalinsu ya zo ba sa jinkirin awa daya, kuma ba sa gabata[14].

 Sannan akwai tambayoyi masu yawa da amsa su zai iya sanya wannan bahasin ya yi tsayi; kamar shin gidan lahira zai koma gida daya ne daga karshe saboda a samu cikakkiyar amsar cewa komai zai kai zuwa ga kamalarsa da ta dace kamar yadda wasu ma'abota irfani suke gani ko kuwa gidajen nan musamman biyu daga ciki wato gidan wuta da na aljanna zasu dawwama ne har abada.

Da kuma tambayar bambancin siffofi da halaye da yanayin rayuwar duniya da ta barzahu da ta lahira, da matsayin jiki da ruhi a wadannan duniyoyi, da kuma bahasin nan na yadda mutum yakan iya cancanjawa yadda ya so a lahira, amma a barzahu yana zama da surar aikinsa ne, a duniya kuwa ba shi da zabi wajen gina kamanninsa domin Allah ne ya halitta masa shi yadda ya so.

Sannan akwai bahasin nau'in abubuwan rayuwa a wadannan duniya da suka hada da tufafi, da abinci, da gidaje, da yadda ake mallakarsu da kuma yanayinsu da kamanninsu da juna. Da kuma bahasin alakar bayi da Allah (s.w.t), da kuma matsayin alakar maza da mata a wadannan duniyoyi, wadanan dukkansu bahasosi ne masu tarin yawa da zasu daukar mana lokaci, sai dai abin da muka kawo ya wadatar zuwa wani lokaci in Allah ya so.

Hafiz Muhammad Sa'id Kano

Cibiyar Al'adun Musulunci Kano Nigeria

hfazah@yahoo.com

2/13/2009



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 next