Ajali KoWa'adi



Ajali KoWa'adi

Sau da yawa akan yi magana kan ajali a matsayin wani abu da Allah ya sanya shi a matsayin hanyar katse rayuwar mutum ta wannan duniyar da ciratarsa zuwa lahira ko kuma duniyar barzahu.

Idan muka duba ajaloli zamu ga sun bambanta ta yadda wasu gajeru ne wasu kuma masu tsayi, sannan kuma wasu ana jinkirta su wasu kuma ana gabatar da su, ta yadda mutum zai iya mutuwa da wuri ko kuma ya mutu ba da wuri ba, da ma'anar cewa yana iya mutuwa ajalinsa na asali bai yi ba, kuma yana iya ketare ajalili masu yawa da ya kamata ya mutu amma sai ya wuce bai mutu ba. Amma ajalin asali dukkan maganganu sun zo a kan cewa ba a iya ketare shi don haka idan ya zo ko babu wani dalili na zahiri to dole ne a wuce.

Sannan tafiya zuwa barzahu ta hanyar ajali ne kawai wanda yake wata haihuwa ce da takan kai mutum wani gida da ya saba wa wannan gida na duniya a dukkan dokokinta da yanayinta, musamman da yake gidan barzahu ya kasu gida biyu ne kawai, koda yake yana iya kai wa gida uku idan mun kira kabarin masu sabo daga musulmi wadanda ba muminai ba a matsayin wani gidan daban. Idan ina son in yi bayani sosai, duniya gida daya ne wanda ba shi da bambanci tsakanin mutane musulminsu da wadanda ba musulmi ba, kuma wannan a fili yake cewa; babu wani bambanci tsakanin wadannan halittun guda biyu, don haka ne ma Allah madaukaki ya sanya ta a bisa asasin riko da sabubba ta yadda duk wanda ya rike sababi to zai samu wannan duniya.

Muna iya ganin ci gaban zamani da ake ganin yana hannun yammacin duniya a yau, wanda a da yana hannun kasashen musulmi ne, hasali ma su kasashen musulmi su suka fara kawo shi suka dankara shi a kan yammacin duniya, amma yau sai ga shi ta juye. Don haka muna iya ganin lokacin da musulmi ya yi riko da sababi a wannan duniya sai ya mallake ta amma lokacin da yammancin duniya ya rike sababi sai ya mallake ta a hannunsa; sai suka zama madogara a karfin soja da tsaro da ilimin fasaha da kere-kere, da siyasa da tafiyarwa, sai suka zama su ne masu hukunci da kotunan duniya da bankuna da dukkan manyan cibiyoyin tattalin arziki. Don haka babu ruwan Allah a matsayin shi na mai arzutawa, yana kwararo arzikinsa ne inda sabubban hakan suka kammala amma wannan fa ba yana nufin ba shi da hannun gaibi na taimako ta wani janibin ba, sai dai lallai muna bukatar riko da sabubba, don haka ne duniya ta kasance gida daya tilo.

Amma a duniyar barzahu gidaje biyu ne kacal, wato "Barhut" da "Wadis salam" sai ya kasance ma'aunin hakan shi ne wanda ya kyautata ayyuka da suka dogara da imani sahihi, don haka ne duk wanda ya yi aiki da Allah ya karba idan ya mutu yana "Wadis salam" ne, wadannan su ne muminai da suka yi aiki bisa jagorancin da Allah ya sanya da shugabanci sahihi da ya yi umarni, kuma su ne wadanda ya shardanta karbar ayyukansu, sai ya kasance da imani ne ake karbar ayyuka, amma da musulunci ne ake auratayya da raba gado da cin yanka da kare jini da dukiya da mutunci, kuma dukkan wanda ya yi musulunci to yana da wannan falala, amma kuma idan bai yi imani ba zai rasa gidan "Wadis salam", wannan wuri a Iraki yake kamar yadda ya zo a wasu ruwayoyi.

Amma wanda bai yi imani ba koda kuwa ya yi musulunci ya yi aiki karkashin wannan musuluncin amma ya yi gaba da waliyyan Allah to da shi da wanda bai yi musulunci ba zasu tsinci kansu a "Barhut" wanda wuri ne da yake a Yaman da Allah ya halicce shi a gabashin duniya da yake da wata rijiya da ake kiranta da "Barhut" kamar yadda ya zo a wasu ruwayoyi. Wannan yana nuan cewa; Barzahu duniya ce mai gidaje biyu kuma ana nufin duk wanda yake "Barhut" zai azabtu, amma kuma wanda yake ya yi musulunci daidai gwargwadon yadda Allah ya yi umarni kamar yadda sako ya zo masa ba kamar yadda Allah ya aiko da sakon ba to Allah ba zai kai shi "Barhut" ba kuma zai huda kabarinsa yana samun sanyin da yake a aljannar da ya halitta a yammacin duniya da ake kiranta "Wadis Salam" da asasinta yake a Iraki, don haka irin wadannan mutane zasu ji dadi a wannan rami na kabari da suke ciki koda kuwa ba a kai su "Wadis salam" ba.

Haka nan duk wanda yake a "Wadis salam" zai ji dadi, domin wuri ne da ake kai wadanda suka yi imani suka yi aiki na gari, wannan yana nuna mana a fili cewa duk wanda yake a Barhut to yana shan wuya, kuma duk wanda yake a Wadis salam yana jin dadi ne. Wannan dai lamari ne da yake da wahalar yin hukunci, kuma akwai tambayoyi da ake ta jefawa kan wannan mas'alar cewa; shin zai yiwu a yi aiki mai kyau ba imani kuma ya samu karbuwa har mai shi ya samu jin dadi a kabarinsa sakamakon yana da uzurin rashi samun sako daidai ko rashinsa gaba daya kamar irin su Hatimud Da'i? ko kuwa zai yiwu a yi aiki maras kyau alhalin akwai imani sai ya kasance shi kuma tun daga kabarinsa yana samun shi ma ni'imar wannan aiki da ya yi sakamakon yana da uzurin rashin samun sako kamar sauran muminai masu zunubi? Ko kuwa zai yiwu a raba aiki mai kyau da imani ta yadda zai kasance yana aiki na gari amma ba mumini ba ne? Sannan kuma shin akwai alaka mai karfi ta lizimtar imani da sanin Allah ko kuwa? Wadannan tambayoyi ne mabambanta da malamai da yawa suka yi sabani kan wasunsu.

Amma idan muka dogara da abin da muka ambata a baya muna iya cewa; Kenan ayyukan mutane su ne ma'aunin jin dadi a Barzahu, sai dai su kasance karkashin imani sahihi ko kuma uzurin rashin samun sako na gari. Kuma idan akwai wanda ya yi imani amma ba shi da aiki na gari to zai sha wahala ke nan sai dai idan ya samu ceton waliyyai daga alayen manzon Allah (s.a.w) kuma wasiyyansa (a.s) kamar yadda wasu hadisai suka yi nuni. Don haka asasin sakamako ya kasance aiki ne mai lasisi daga Allah, don haka wanda bai yi samu sako ba ko bai zo masa daidai ba, amma ya tsayar da adalci tsakanin mutane, ya yi kyauta bai yi keta da hassada ba, bai cuci kowa ba, bai hada sharri ba, ya kiyaye hakkokin mutane to zai samu jin dadi, amma wanda bai yi ayyuka na gari ba koda kuwa ya yi imani to zai samu fuskantar matsaloli. Sai dai kamar yadda muka kawo akwai maganganu masu yawa kan mas'alolin "Barzahu" da ba mu da isasshen lokacin tattauna su a wannan makala gajeriya.

Amma lahira sai ta kasance ita ce haihuwa ta uku ta mutum kuma fadinta ya fi na barzahu kamar yadda fadin ciki yake ne da bambancinsa da wannan duniya haka ma fadin duniya yake tsakaninsa da na barzahu, sannan kuma tsakanin fadin barzahu da lahira da za a koma gaba daya kamar nisan da yake tsakanin fadin duniya da barzahu ne, don haka ita wuri ne da ba shi da iyaka.

Lahira tana da gidaje uku ne da suka hada da; gidan wuta, da na aljanna, da wata duniyar daban a gidan wuta amma ita tana da ni'ima ne, sai dai ni'imarta ba ta kai ta aljanna ba, domin ita aljanna ba ta da iyaka kuma sakamakon imani ce, don haka lahira sai ta kasance duniyoyi uku ne, sai dai maganganu suna kaikawo kan cewa irin wadannan mutane za a aika musu da dan sako ko tun a Barzahu ko kuma a wannan duniya domin a jarraba su sai a kai wadanda suka yi ban gaskiya aljanna wadanda kuwa suka karyata a kai su wuta.



1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 next