KebantattunAl’amuran Mahangar Shi'a



“Kada ku yi barna a bayan kasa bayan gyara ta”. A’arafi: 56[14].

Daga cikin wasikar da imam Mahadi (A.S) ya aika wa shaikh Mufid yana cewa: “Kowannenku ya yi aiki da abin da zai kusantar da shi zuwa garemu, ya sanya soyayyarmu gareshi, ya nisanci duk wani aiki da yake sanya rashin yardarmu, domin al’amarinmu zai bayyana ne bagatatan[15].

Boyuwarsa ta yi kama da ta annabawa don haka muka ga shaihul Saduk yana kawo boyuwar annabawa kamar; Idris, Salihu, Nuhu, Ibrahim, Yusuf, Musa da wasiyyansu, yana kawo bayanin boyuwarsu a babin boyuwa a littafinsa na “Kamaluddin wa tamamun ni’ima”[16]

Kur’ani mai girma ya yi bayanin boyuwar annabawan da suka gabata kamar Khidr (A.S) wanda boyuwar imam Mahadi (A.S) ta yi kama da boyuwarsa fiye da kowacce. Boyuwa ce da saboda mu’ujizar kur’ani ba wanda ya iya musun ta.

Wanan kissa da Khidr (A.S) da Musa (A.S) ta zo a cikin surar Kahafi[17] wacce take kunshe da muhimman abubuwa kamar haka:

1- Boyuwar Khidr da rashin saninsa duk da kuwa yana rayuwa a cikin mutane, ba don Allah ya yi bayaninsa ba, ba wanda zai san shi.

2- Kamar yadda Khidr (A.S) yake sane da mas’alolin al’umma da na duniya kamar yadda ya san cewa shugabanni suna kwace jiragen ruwa marasa aibi don haka ya aibata shi, haka nan imam Mahadi (A.S) yake sanin al’amura da halayen duniya na raunanan mutane dalla-dalla.

3- Kamar yadda lalata jirgi da Khidr ya yi ya zamanto a boye ne, domin da masu jirgi sun gan shi da sun hana shi yin hakan, haka ma imam Mahadi (A.S) yake tasarrufi a boye cikin al’amura masu yawa ba tare da mutane suna ganinsa ba.

4- Shiryar da Annabi Musa (A.S) ga wasu al’amura ta hanyar Khidr (A.S), wato gina mutum da aiwatar da sakon Allah, haka ma imam Mahadi (A.S) yake gina mutane yana aiwatar da sakon Allah a boye[18].

Don haka ne imam Mahadi (A.S) bayan kare mazhaba da yake yi daga rushewa da kaucewa kuma shi ne akwatin sirrin Allah mai tarbiyyantar da mutane a boye a duniya.



back 1 2 3 4 5 6 next