Hakkokin Soyayya



Hakkokin Soyayya

Hujjatul Islam Muhammad Raishahari

Hafiz Muhammad Sa’id Kano

8 / 1

Himmantuwa Da Hakkokin ‘Yan’uwa

293. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: a cikin wasiyyarsa ga dansa Muhammad dan hanafiyya: ya kai dana… kada ka tozarta hakkin dan’uwanka haka nan kawai kana mai dogara da alakar da take tsakaninka da shi; ka sani wanda ka tozarta hakkinsa ba dan’uwanka ba ne[1].

294. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: ka kasance mai kiyayewa ga so, koda ba ka sami mai kiyaye wa ba[2].

295. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: mafi kyawun mutunci shi ne kiyaye soyayya[3].

296. Daga Imam Ja’afar Sadik (A.S) ya ce: Allah madaukaki yana kiyaye wa ga mai kiyaye abokinsa[4].

8 / 2

Hakkokin ‘Yan’uwa

a- alfarmar rai da dukiya

297. Daga Manzon Allah (S.A.W) ya ce: ku saurara ya ku mutane, hakika musulmi dan’uwan musulmi ne da gaskiya[5].

b- Mayar Da Gaisuwa

298. Daga Manzon Allah (S.A.W) ya ce: hakika musulmi dan’uwan musulmi ne idan ya hadu da shi sai ya mayar masa da sallama kwatankwacin yadda ya yi masa ko mafi kyawu daga hakan[6].



1 2 3 4 5 6 next