Muhammad Manzon Allah



Wanene Muhammad (S.A.W)

Muhammad shi ne annabin da Allah a aiko shi a matsayin annabin karshe domin shiryar da dukkan halitta gaba daya.

A lokacin da aka haife shi Makka da Dakin Allah sun kasance a cike da daudar bautar gumaka, sannan kuma Yahudawa da Kiristoci suna rayuwa a Jazirar larabawa.

Daular Farisa tana mallakar gabashin jazirar larabawa, kuma ga daular Rumu a yammacinta maso arewa, kuma da daula ta uku ta Habasha a yamma, kuma a kudu akwai Daular Yemen da ta kasance karkashin mulkin mallakar Habasha a lokacin haihuwar annabi, da kuma Tekun Indiya.

An ambaci shekarar haihuwarsa da “Shekarar giwaâ€‌[1], saboda harin da Habasha ta kai wa Ka’aba domin rusa ta a wannan shekarar. Kuma abubwan mu’ujiza sun wakana yayin haihuwarsa (S.A.W) da suka hada da:

1.     Faduwar gumaka akan fusakunsu

2.     Rushewar katangun kisira da suke Shiraz

3.     Mutuwar wutarsu da suke bautawa

4.     Kafewar kogin Sawa

a.      Dukkan wadannan abubuwa sun faru ne a shekarar miladiya ta 571 ne[2].



1 2 3 next