Bidi’a A Cikin Addini



 

Bidi’a A Cikin Addini

Kamar yadda yake kafa doka hakki ne kawai na Allah madaukaki sannan babu wani wanda yake da wannan hakkin ta yadda zai kafa wa wani mutum kowata al’umma doka. Haka nan babu wani wanda yake da ikon ya kara ko ya rage wani abu a cikin dokokin da Allah a saukar ta hanyar wahayi. Saboda haka sanya hannu a cikin dokokin da Allah ya saukar ta hanyar ragi ne ko kari, wannan shi ne ake kira da “Bidi’a” a cikin addini. Saboda haka mutumin da ya yi haka ya yi bidi’a a cikin kadaita Allah a cikin kafa doka wanda muka yi maganarsa a sama.

Sakamakon barnar da ke akwai wajen (bidi’a) ko sanya hannu wajen kafa doka ya zamana daya daga manyan zunubbai wanda wannan bahsin da muke cikinsa yake dauke da cikakkiyar ma’anar “Bidi’a” wanda yake daya daga cikin muhimman abubuwan da zamu yi magana a kai nan gaba.

Ma’anar Bidi’a a harshen larabci shi ne, yin wani abu sabo wanda yake da ba a yinsa. Saboda haka duk wani sabon abu wanda yake da ba a yinsa ana kiransa “bidi’a”. [6]

Dabi’ar Mafi yawan mutane Suna son sabon abu, sannan ba su son rayuwar da take da yanayi iri guda babu canji. Sakamkon haka ne ya sanya masana ginin gidaje a kodayaushe suke kokari wajen samar da zane da nau’oi’in gidaje kala daban-daban, sannan kalar tufafin da mutane suke sanyawa kullum yana samun canji, dukkan wadannan ta fuskar lugga ana kiran su da Bidi’a. A kan haka ne ma Kur’ani mai girma yake ambatar Allah madaukaki da “Mai kirkiro sammai da kassai”[7]. Domin kuwa shi ne ya kirkiro sammai da kasai ba tare da ya ga makamantansu ba kafin nan, Wani abu ne sabo wanda a da bai gabata ba.

Amma a nan akwai wani abu wanda ba mu fada ba dangane da ‘bidi’a’ domin kuwa bidi’a da wannan ma’ana ba ita ce ba ce muka yi magana ba a kanta a bahsin mu na baya wacce take an haramta kamar yadda muka yi bayani.

Domin kuwa musulunci ba ya hani a kan sababbin abubuwa a cikin rayuwar daidaiku da zaman tare. A yau dan Adam dangane da yanayin rayuwrsa yana da abubuwa sababbi wadanda ba a taba yinsu a tarihi, kamar abin da ya shafi gine-gine da tufafi da dai makamantansu. Duk da cewa wadannan a mahangar ma’ana ta kalmar ‘Bidi’a’ suna iya shiga a ciki amma ba su daga cikin bidi’a wacce ake magana wacce take daya daga cikin manyan zunubbai.

A cikin tarihi ana rubutawa cewa farkon bid’ar da sahabbai suka zo da ita bayan wafatin Manzo shi ne tankade garin alkama, wannan al’amari ne wanda yake sabo kuma da ba a yinsa, amma wannan ba ya daga cikin bid’ar da malamn fikihu suke cewa tana daga cikin manyan zunubbai. Saboda haka dole a bayyanar da cikakkiyar ma’anar bida’r da ake magana a cikin shari’a.

Amma bid’ar da malaman fikihu da akida suke magana a kanta kuma take daya daga cikin manyan zunubbai ita ce shigo da wani abu a cikin addini ta hanyar rage wani abu ko kuwa kara wani a cikin addini wanda bai zo ba daga Allah. Misali kamar yadda a kara wani abu a cikin kalmomin kiran salla ko kuma rage wani abu daga ciki. Ko kuma kara lokaci ko rage shi a cikin lokacin azumi sabanin yadda adini ya zo da shi wato daga bulluwar alfijr zuwa faduwar rana.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 next