Tattaunawa Ta Bakwai



Amma batun hadisan da suka yi magana kan sahabbai da kake cewa a yi adalci a hada biyun sai in ce maka: In ganin yana da kyau ka yi wa kanka adalci, ka kawo me kake nufi, bai kamata ka kasa kawo su wa ake nufi ba, kuma ka sani addini yakan zo da dokoki ne, idan wadannan dokoki wani ya siffanta da su sai su hau kansa.

Idan ka duba da mai gani zaka samu wadannan hujjoji a fili kuma mun gabatar maka da su tun tuni, sannan kana iya karawa da wannan: Kifayatul asar: shafi: 134: inda aka yi nuni da matsayin Ali kamar Haruna da Musa (a.s) ne, da wasiyya da imamai goma sha biyu. Sharhu Ihkakul Hakk: j 13, Mar'ashi Najafi: 78: a cikin akwai magnar Fakhrur Razi da take nuna ismar Ulul amr da dogaro da wannan ayar da cewa su ma'asumai ne ba sa sabo. Sanna ka duba Zamakhshari: Manakib; 213. da Hamwini: fara'idus Simdain. Da Kanduzi a Yanabi'u: shafi: 82, Istambul. Da: sauran masdarori masu yawa matuka. Kamar Sawa'ikul Muhrika: 234. Nahajul balaga: j 2, shafi: 27. Ibn Abil Hadi: j 9, shafi: 313.

Amma game da hana mummuna ko umarni da kyakkyawa sai na ce maka; Ka sani umarni da kyakkyawa yana da sharudda idan sharudda suka fadi to ya saraya inda suka fadin. Ka duba yadda ka fada kana mai dogaro da hankali sahihi shine dole ne duk sadda kaga abin da ba daidai ba in har zaka iya kokarin gyara, to dole ne kayi. Sa'annan kana amafani da mutlakat a ko'ina ko amfani da ra'ayi wurin fassara: Ka sani "Khairu ummatin" imamai ne ma'asumai (a.s) mu kuma mu ne "nasi". Su ne wadannan da Allah madaukaki ya yi mana ni'ima da fitar da su garemu domin mu yi musu biyayya. Su ne "Ummatan wasadan" kuma mu ne "nasi" mutanen da zasu yi sheda a kanmu cewa mun bi ko mun ki umarnin Allah na biyayya garesu.

Wallahi khairu ummatin su ne (a.s)! yaya sauran mutane zasu kasance Khairu ummatin alhalin wannan  al'ummar ta Annabi (s.a.w) ta kashe shi kuma ta kashe jikokinsa kuma wasiyyansa gaba daya, fiye da kisan da yahudawa suka yi wa wasiyyan Annabi Musa (a.s) mu ne (Nasara ma suka yi wa wasiyyan Isa (a.s))!

Suyudi ya ruwaito cewa: Ahlul bait (a.s) ake nufi da su a tafsirin wannan ayar. Da sauran littattafan Sunna da Shi'a masu yawa da suka nuna ma'anar da manzon Allah (s.a.w) ya bayar.

Wasu Abubuwan La'akari: Ina ganin babbar matsalarka ta farko tana cikin rashin sanin hakikanin Allah (s.w.t) da manzonsa (s.a.w) ne. Allah madaukaki da a koyarwarku aka dauke shi da matsayin siffofi da ba su cancanci she ba, ina ganin koma wa da saninsa yana da muhimmanci gareka: wadannan siffofi da kuka ba wa Allah madaukaki da suka hada da:

Kamarsa da Annabi Adam (a.s) da tsayinsu irin daya: (fatawa bn Baz, j 4, shafi: 226). Kasancewarsa wani saurayi ne mai takalma biyu, mai gashi har baya, da korayen kafafu, yana da takalman silifa biyu na zinare, da wata ado ta zinare a fuska. (Ta'alikin Albani ga sunnar ibn Abi Asim No. 471)

Zaman Ubangiji kan al'arshi kuma yana da girma daidai al'arshin ne, sai dai al'arshin ya fi shi girma da kadan kamar girman 'yan yatsu hudu ne. (firdausil akhbar, j 1, shafi: 219). A littafin Akadul farid (j 6, shafi; 208) kuma macijiya ta kanannade al'arshin. Wannan kuwa yana nuna ta fi al'arshin tsawo sosai.

Zaman Allah kan kursiyyu: (tafsiru Dabari: j 3, s: 7)

Al'arshinsa kuwa yana kan dabbobi ne, daya mutum daya sa, daya mikiya, daya zaki. (hayatul haiwan, j 2, s: 428) da (Jahiz, kitabul haiwan, j 6, shafi: 221). Da wasu littattafai kamar al'isaba 549. tafsirud Dabari.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 next