Tattaunawa Ta Biyar



Amma game da abin da aka yi wa alayen Annabi (s.a.w) ina mamakin jahiltar ka ga addini: Idan ka yi musun tarihin la’antar Imam Ali (a.s) to lallai ka nuna wa duniya rashin saninka da tarihin addininka sannan kuma ka jahilci musallamat na tarihi da al’umma ta hadu a kai. Amma Imam Hasan (a.s) bai bayar da iko hannun Banu Umayya ba, sai dai abu ne wanda ya zama masa tilas kamar yadda dukkan imamai (a.s) suka yi hakuri kan abin da ya fi karfinsu. A yanzu zaka iya cewa manzon rahama (s.a.w) ya bar mulki ga mutanen makka ne bisa sonsa, ba don saboda ba shi da karfin da zai iya kwata daga hannunsu ba?!

Sannan da kake cewa ya kamata a yi shiru kan abin da ya faru: Inda abin da ya faru ya kamata a yi shiru kansa da Kur’ani ya koyar da mu hakan: sabanin hakan Kur’ani ya karfafi mu binciki abin da ya faru baya domin kada mu fada irinsa, sannan kuma manzon rahama (s.a.w) da wasiyyansa (a.s) duk sun koya mana hakan; Wannan doka da Basari da Nu’uman suka sanya ta saba da Kur’ani da hadisai ingantattu kuma ba yadda za a yi ta fitar da mu matsalolinmu na duniya da lahira.

Ka sani binciken tarihin da ya gaba ta, ba don a gano laifin wani ba ne, sai dai domin ka san waye yake hujja kanka ka bi shi da wanda yake ba hujja ba, domin yanzu muna iya tambaya cewa; waye yake hujja ne bayan Annabi (s.a.w) a kanmu mu karbi addini daga gareshi waye kuma ba hujja ba?! Ku kun dauka domin a ce wane ya yi laifi ne, wane kuma bai yi ba shi ke nan. Idan kuwa haka ne da ba shi da amfani, da Kur’ani bai yi binciken halayen wadanda suka gabata ba?.

Amma abin da

Amma game da Hakim da ya fitar da hadisin da ya san Buhari da Muslim sun yarda da shi, sai dai Buhari bai kawo shi ba, da kuma musun matsayin Hakim: Idan ka yi kokwanto kan Hakim to ka nuna jahiltarka da sunnanci. Amma da ka ce Manzo (s.a.w) ya bar duniya yana kan Kur’ani da hikima haka ne mana, amma wannan yana nuna abin da Manzo (s.a.w) ya yi ne, ba ya hana kuma cewa ya bar wa al’umma Littafin Allah da Ahlul Bait (a.s), ko kana da jur’ar da zaka ce da ya tafi sai ya tafi da kur’anin da hikimar bai bar wa al’ummarsa su ba ne! kuma mun sha nanatawa cewa Allah ya yi alkawarin kare kur’anin ne. amma Sunna abin da yake cikinta musamman ma maganganunsa ya gabata cewa; akwai wanda aka jingina masa, kuma tun yana raye aka fara yi masa karya, ka ga ke nan ina ga bayan idanuwansa (s.a.w).

Amma game da Halifofi sha biyu: Ya gabata mun ba ka madogara da ka yarda da ita kan halifofi goma sha biyu ne. kuma sanadin hadisin a gun Muslim shi ne dai ya zo a gunmu a littafin Kafi, sai dai ku kun ce dukkaninsu daga Kuraish ne, amma a gunmu dukkaninsu daga Banu hashim ne, Jabir ya yi furuci da cewa an yi kokarin canja karshensa har da neman boyewa, al’amarin da yake nuna Banu hashim ne daidai sai aka jirkita shi da kuraish domin ya game kowane irin bakuraishe. Haka nan Shiblanji mai Nurul Absar ya kawo tarihinsu gaba daya, bayan ya kawo na halifofin farko uku, ka koma wa littafinsa.

Amma fadinka: "Ba zan taba yadda da cewa babu alaka tsakanin son mutun da son ahalinsa ba": Shin ba ka fahimtar abin da kake cewa ne, dubi yadda ka yi magana sai kuma a karshenta ka warwareta. Kana cewa ne: akwai alaka tsakanin son mutum da son ahlinsa, sai kuma ka kawo yadda Annabi guda ya ki dansa kana mai warware jumlar baya.

Amma batun da kake neman shigar da wasu cikin Ahlul Baiti (a.s) wanda manzon Allah bai shigar da su ina ganin amsar da zan ba ka kamar haka: Don Allah ka rika kula da abin da kake cewa:

Na daya: Annabi (s.a.w) ne ya kore matansa daga Ahlul Bait (a.s) ba ni ba. Na biyu: Zaid bn Arkam ne yake da wannan ra’ayi cewa: su ne aali Ali (a.s) aali Abbas aali ja’afar da aali Akil, ba Annabi ba.

Aikin Annabi (s.a.w) doka ce mai karfi da ba mai ture ta sai munafiki ko kafiri, don haka idan Annabi (s.a.w) ya yi wani abu, to mu ba mu da wata doka da zamu kirkiro ta ture ta sai dai mu sallama.



back 1 2 3 4 5 6 next