Tsarin Siyasa A Musulunci



Me kuwa zai sanya dan’adam ba zai wahala ba alhalin ya kauce wa tsarin da zai fisshe shi daga bala’in duniya da lahira, mu sani duk duniya babu wani wuri da ake bin tsarin addinin musulunci kamar yadda Allah (S.W.T) da manzonsa (S.A.W) suka zo da shi, wani wurin ana gaba da addini ne, wani wurin kuma ana jahiltarsa ana yin wani abu daban da sunan addini amma addini ba haka ya ce ba, ba komai ake yi ba sai fahimtar mutanen wurin game da addini. Wani wurin kuma an fahimci addin kamar yadda manzo (S.A.W) da wasiyyansa (A.S) suka zo da shi, amma fa al’adu sun hana a aiwatar da shi. Wannan sai ya sanya duk duniya ba inda ake yin addini koda kashi 50% cikin dari a duk fadin wannan duniyar.

Wasu sun dauka an zo duniya domin shan wahala ne don haka sai suka dauka wahalar da ake sha da ma haka duniya take! wannan lamarin kuwa ya taso daga jahilcin dan’adam ne, ko kuma daukar da ya yi wa abin da yake faruwa kamar daman haka ya dace ya faru! Mu sani duniya da lahira duka an yi su domin samun kamalar dan’Adam ne, bambancin al’amarin shi ne akwai wahalar ibada a wannan duniya. Kuma rashin lafiya da cututtuka duka Allah ya bayar da maganinsu sai dai dan’adam ya nisanci wanda zai yi masa maganin ne. Sannan muna ganin yadda manzon Allah (S.A.W) da imam Ali (A.S) suka yaki talauci da yunwa ta karfin tsiya da kuma kawo aminci da ilimi da tarbiyya da sauransu. Imam Ali (A.S) yana cewa: Da talauci mutum ne da na kashe shi (Sharhu Ihkakul hakk: J 32, shafi: 257)

Arzikin duniya ya ishi dan’adam amma ya wanzu a bankunan masu mulki da iko ana boye shi ana juya shi, kuma wannan lamarin shi ne abin da Allah ya yi gudunsa yana mai cewa; “…domin kada ya kasance yana juyawa tsakanin mawadata daga cikinku…”(Hashari: 7), amma dan’adam da aka yi arzikin saboda shi sai ya kwana cikin yunwa da musibu da talauci.

Amma batun cewa; me ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan annabi (S.A.W) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa?

Kuma me ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan annabi (S.A.W) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa?

3- Amma abin da ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan annabi (S.A.W) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa shi ne ta koma zuwa ga koyarwarsa, ta san wane ne shi sannan sai ta san wadanda ya ce ta koma musu wajen sanin addininsu, to da wannan ne zasu iya zama ‘yan jam’iyyar Allah madaukaki.

Da wannan ne zasu koma zuwa abin da ya fada a littafinsa: “Kawai hukunci na Allah ne” (al’an’ami: 57). Da fadinsa: “…Hukunci nasa ne…” (al’kasas: 88). Da kuma dukkan ayoyin da suka yi nuni da fasikanci ko kafirnci ko zaluncin wanda bai yi hukunci da abin da Allah ya saukar ba, da wannan ne sai su aikta ayyukan da suke kansu na mu’amala da dukkan wani dan’adam bisa yadda shari’a ta ce musu kamar yadda ya zo daga wajen Allah madaukaki. Sai ya kasance alakokinsu da kowa bisa yadda Allah ya so ne kuma jagoransu na wannan zamani ya tsara ya nuna musu. Da wannan ne zasu kasance ‘ya’yan jam’iyyar Allah madaukaki wacce take da sakamakon yardarsa duniya da lahira.

Irin wadannan malamai da suke bin tafarkin Allah madaukaki da manzonsa (S.A.W) da wasiyyansa (A.S) su ne wadanda manzon rahama (S.A.W) yake cewa: “…hakika malamai magada annabawa ne” (kafi: j2, sawabul ilm, hadisi: 1) da fadin imam Ali (A.S) cewa; “Malamai su ne masu jagorancin mutane” (Gurarul hikam: 137), da fadin manzon Allah (S.A.W) da yake nuna cewa; idan malamai suka bata to zasu batar da wannan al’umma.

Wani abin mamaki shi ne yadda wasu malamai suka ki fahimtar al’amarin jagoran al’umma bisa gurbatacciyar fahimta sakamakon kaucewa wasiyyar da annabi (S.A.W) ya yi na su bi abin da yake kunshe cikin Kur’ani bisa fahimtar  ahlin gidansa (A.S) wadanda Allah madaukaki ya tsarkake su kuma manzon Allah (S.A.W) bai bar wannan duniya ba sai da ya yi wasiyya da su kamar yadda muka yi nuni a baya da halifofinsa goma sha biyu ne kamar yadda ya kawo su kuma ya yi wasiyya da su.

Wani abin mamaki shi ne yadda wasu sukan yi kokarin su boye wasiyya ko su yi musunta, ko kuma su daukar wa kansu yarda da cewa; manzon Allah (S.A.W) ya fadi sha biyu amma bai kawo sunayensu ba, don haka sai su shiga neman kawo sunayen da kansu kamar dai Allah ya yi wahayi cewa; manzonsa (S.A.W) ba zai cika addininsa su ne zasu zo daga baya su cika. Irin wannan son rai yana nan kunshe cikin littattafai daga wasu masu irin wadancan mahanga ta su cika addini da kansu! Allah ya tsare mu tabewa!



back 1 2 3 4 5 6 7 next