Tsarin Siyasa A Musulunci



Amma tun da al’umma sun kauce wa siyasar Allah (S.W.T) da manzonsa (S.A.W) da wasiyyansa (A.S) kuma jam’iyyarsu mai cike da tsiran dan’Adam a duniya da lahira wacce take jam’iyya ce ta imani na gaskiya, to mene ne hukuncin sauran jagorori da ake rikonsu a matsayin shugabanni? Kuma mene ne sakamakon da ya samu al’umma sakamakon kauce wa siyasar Allah (S.W.T) da jam’iyyarsa. Kuma me ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan annabi (S.A.W) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa?

Wannan sai ku biyo mu ba shi idan Allah ya sa mun samu lokaci a nan kusa…

Amma tun da al’umma sun kauce wa siyasar Allah (S.W.T) da manzonsa (S.A.W) da wasiyyansa (A.S) kuma jam’iyyarsu mai cike da tsiran dan’Adam a duniya da lahira wacce take jam’iyya ce ta imani na gaskiya, to mene ne hukuncin sauran jagorori da ake rikonsu a matsayin shugabanni? Kuma mene ne sakamakon da ya samu al’umma sakamakon kauce wa siyasar Allah (S.W.T) da jam’iyyarsa. Kuma me ya kamata wannan al’ummar ta yi game da jagoran gaskiya kuma halifan Annabi (S.A.W) na sha biyu da yake wannan ne zamaninsa?

Musulunci addini ne na tsari wanda bai yarda dan’adam ya zauna haka nan babu daula ba, don haka ne ma ya kasance ya dauki matakin kiyaye tsarin rayuwar al’umma da yake akwai maslaharsu a ciki, sannan kuma sai ya shimfida dokokin da yake kiran su hukunci na biyu wadanda sun saba da na asali. Ina ganin domin fahimtar wannan al’amari yana da kyau mu kawo misalan wasu kissoshi da suka zo a littattafan addini:

1. Wata rana Annabi Ibrahim (A.S) yana tafiya a gaban gwamnan da ya so ya kwace matarsa amma ya kasa, wanda daga baya ya ba shi kyautar Hajara babar Annabi Isma’il (A.S) sai suka fito suna tafiya gaban farfajiyar fadar gwamnan, sai Annabi Ibrahim (A.S) ya shiga gabansa yana tafiya, sai Allah madaukaki ya yi masa wahayi cewa; ya kai Ibrahimi (A.S) ka sani babu makawa al’umma ta samu shugaba Nagari ne ko fajiri; abin da ake nufi da nagari a nan Shi ne wanda Allah (S.W.T) ya zaba a shar’ance a matsayin jagoran al’umma, fajiri kuwa yana nufin duk wanda yake ba bisa wannan ka’ida ba.

Sai gwamna ya ga Annabi Ibrahim (A.S) ya koma bayansa yana tafiya, sai ya tambaye shi me ya sa na ga ka koma bayana, sai ya ce: ubangijina ne ya yi mini wahayi da in girmama ka. Wannan al’amarin ya sanya shugaban ya ga girman Ubangijin Ibrahim (A.S) har ya karkato zuwa gareshi.

Kissar Annabi Yusuf (A.S) ba nesa take da mu ba, a cikin kur’ani mai girma yayin da ya nemi a ba shi ministan arziki da albarkatun kasa, don haka ne ma wani wanda ya yi wa imam Rida (A.S) rashin kunya yana zarginsa da shiga  fadar sarki Ma’amun dan Harunar Rashid, sai imam Rida (A.S) ya ba shi amsar da ta sanya shi yin nadama, yana mai nuna masa cewa; tsakaninsa (A.S) da Annabi Yusuf (A.S) ya zabi wanda ya fi laifi a wurinsa yayin da shi imam Rida ya karbi sarautar Yarima ne bisa tilas, amma Annabi Yusuf (A.S) ya nemi ministan arziki da albarkatun kasan Misira yana mai rokon sarki ya ba shi wannan matsayi, sannan kuma Imam Rida (A.S) ya kasance a fadar musulmi ne masu shaidawa da Kadaitar Ubangiji madaukaki, yayin da Annabi Yusufi (A.S) ya zauna a fadar mutane ne da suke bauta wa gumaka!

A nan ne zamu ga muhimmancin kare tsarin al’umma da kuma yin hidima ga al’umma da kiyayewa bisa adalci, mu sani imam Ali (A.S) yana cewa: “Mulki yana wanzuwa tare da kafirci amma ba ya wanzuwa tare da zalunci”. (sharhi usululkafi: Mazandarani, j 9, s 300.

Sai dai wani yana iya tambaya cewa; me ya sa wadannan manyan bayin Allah (S.W.T) guda uku: Annabi Ibrahim (A.S) da Annabi Yusufi (A.S) da imam Rida (A.S) suka dauki wadannan matakai, ashe ba hakkinsu ba ne su rike jagorancin al’umma sai kuma suka dauki wadannan matakai a gaban wadannan sarakunan lokutansu?

Sai mu ce: matakai ne da suke sassabawa da sabawar yanayi, don haka ne ma hukuncin Allah a kowane fage da ya hada da siyasa yake sassabawa, misali da Imam Hasan (A.S) ya zo lokacin Imam Husain (A.S) da zai yi yaki ne da Yazid, kamar yadda da imam Husain (A.S) ne a lokacin Imam Hasan (A.S) to da zai yi sulhu da Mu’awiya. Don haka ne mukan ga wani lokaci Annabi (A.S) ko Imami (A.S) ya dauki matakin da ya saba da na waninsa (A.S) kamar matakin Annabi Isa (A.S) a daular Rum da ya saba da matakin Annabi Musa (A.S) a daular Misira kafinsa da kusan shekaru 1100. Ko kuma Annabi daya ya daukin matakan siyasa da suka saba a lokuta biyu kamar yadda Annabi Ibrahim ya kira sarkin Babil a kan Tauhidi har ya kona shi, amma sai kuma bai yi wannan kiran ba ga sarkin Siriya da na Misira. Kuma muna iya ganin Imam Ali ya yi hakuri ya zauna lafiya da halifofin farko bai dauki matakin yaki ba, amma sai ya dauki wannan matakin tare da Mu’awiya, wanda da ya kyale tabbas da ya zama shugaba a zamaninsa shi ma bayan Usman dan Affan, kuma a zahiri yake wadannan matakai sun sassaba.



back 1 2 3 4 5 6 7 next