Sabuban Soyayya



h- Ladabi

66. Imam kazim (A.S): Kada ka kawar da jin kunya tsakaninka da dan’uwanka, ka wanzar da ita; domin idan ta tafi, kunya ta tafi, kuma wanzuwar jin kunya shi ne wanzuwar kauna[25].

i- Kauna

67. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Da kaunar juna ne ake karfafa soyayya[26].

68. Imam Muhammad Bakir (A.S) ya ce: Wani mutumin kauye daga banu tamim ya zo wajen Annabi (S.A.W) sai ya ce masa: yi mini wasiyya. Ya kasance daga abin da ya yi masa wasiyya shi ne: ka soyu zuwa ga mutane zasu so ka[27].

j- Kaskanda Kai

69. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: soyayya ita ce sakamakon kaskanda kai[28].

K- Cikawa Da Alkawari

70. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: cika alkawari yana kawo shakuwa da juna[29].

l- Adalci

71. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: adalci yana kawar da sabani, yana kuma kawo shakuwa da juna[30].

72. Daga gareshi (A.S) ya ce: Adalci yana dawwamar da soyayya[31].

73. Daga gareshi (A.S) ya ce: Mai adalci yana da yawan masoya da masu kauna[32].

m- Gaskiya

74. Imam Ali (A.S) ya ce: mai gaskiya yana samun abubuwa uku: kyautata amintuwa da shi, da sonsa, da kuma jin kwarjininsa[33].

n- Tausasawa

75. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: wanda dabi’arsa ta tausasa, to sonsa ya wajaba[34].



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 next