Sakon Ali a.s ga Malik Ashtar



Sak'on Imam Ali (a.s) Zuwa ga Malik Ashtar
Na: Imam Aliyyu Al’Murtadha (a.s)
Tarjamar::   Hafiz Muhammad Sa'id
Mai Yad'awa: Cibiyar Haidar don Yad’a Musulunci
Bugu Na Farko:   1433, 20012, 1391
Gurin Bugawa:  Kano
Adadi:    10000
Email:     hfazah@yahoo.com
 
Da Sunan Allah Mad'aukaki
Godiya ta tabbata ga Allah (s.w.t)
Aminci ya k'ara tabbata ga bayinsa wad'anda ya zab'a
"Kawai Allah yana son ya tafiyar da daud'a daga gareku ne Ahlul Baiti kuma ya tsarkake ku tsarkakewa " .
"Lallai ni mai bar muku nauyaya biyu ne; Littafin Allah da Ahlin gidana, ba zaku tab'a b'ata ba bayana har abada matuk'ar kun yi rik'o da su " .
Kuma sama ya d'aukaka ta, kuma ya sanya sikeli. Kuma ku daidaita awo da adalci, kada ku rage sikelin. Kuma k'asa ya sanya ta domin talikai ne .
 
Gabatarwa
Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai
Tsiran Allah da amincinsa su tabbata ga annabi Muhammad Al-mustafa (s.a.w) da alayensa tsarkaka
Wannan shi ne sakon da Imami Sayyidi Ali dan Abu Dalib ya aika zuwa ga Malik Ashtar, da ya tura a matsayin wakilinsa (gwamnansa) a Misra, wanda kafin ya kai zuwa gareta ne Mu'awiya dan Abusufyan ya aika wanda ya sanya masa guba a zuma ya sha ya mutu a hanya.
Wannan sako ne na kundin tsarin aiki ga duk wani jagora ga kansa da al'ummarsa don sanin yadda zai yi jagoranci nagari da mu'amala mai kyau ga jama'arsa.
Mustashrikun (Turawan yammancin duniya kwararru kan ilimin sanin addinin musulunci) sun himmantu da wannan sakon, kuma a kasar Jamus sun tarjama shi zuwa yarensu suka sanya shi "Dokar Asasi" da ake dogaro da shi a matsayin "Makomar Doka".
Kamar yadda a Kenya an tarjama sakon zuwa yaren Suwahili aka aika shi ga shugaban kasar (wanda yake Kirista ne), sai sakon ya kayatar da shi ya yi umarni a raba shi ga dukkan gwamnoni da manyan ma'akatun kasar, ya kuma yi kalamai da suke nuni ga cewa; da sun san wannan sakon tun da wuri, da ba su kasance a yadda suke ba.
Haka nan Majalisar dinkin duniya ta aika sakon ga sarakunan kasashen larabawa tana tunatar da su cewa akwai mamaki cewa suna da irin wannan sakon amma ba sa yin aiki da shi don warware dukkan wata matsala da ta addabi dan Adam!
Sayyidi Ali shi ne na farkon jagororin Ahlul-baiti guda goma sha biyu da manzon Allah (s.a.w) ya yi umarni da riko da su tare da littafin Allah bayan wafatinsa kamar yadda ya zo a manyan littattafan ruwayoyi na hadisai. Sai dai kauce wa wannan wasiyya ta manzon Allah (s.a.w) ya sanya al'umma fadawa cikin rudani da bambance-bambance har zuwa wannan zamanin.
Allah (s.w.t) yana fadi a littafinsa game da alayen manzon Allah (s.a.w) cewa:
"Kawai Allah yana son ya tafiyar da dauda daga gareku ne Ahlul-baiti kuma ya tsarkake ku tsarkakewa" .
Wasiyyar manzon Allah (s.a.w) ga al'ummarsa:
"Lallai ni mai bar muku nauyayan (alkawura) biyu ne; Littafin Allah da Ahlin gidana, ba zaku taba bata ba bayana har abada matukar kun yi riko da su" .
Hadisai sun yi nuni da su a littattafai daban-daban, kamar yadda Shehu Usman dan Fodio Allah ya kara masa yarda ya kawo sunansu a cikin Nasihatu Ahlizzaman a yayin da yake kawo salsalar Imam Mahadi (a.s) wanda zai zo a karshen duniya. Da al'umma ta fuskanci koyarwarsu, da ba ta samu kanta cikin wannan faganniya da rudani ba, sai dai abin da ya faru ya riga ya wakana.
Domin tubarraki zamu kawo sunyensu kamar haka: Imam sayyidi Ali (a.s), sai Imam Hasan (a.s), sai Imam Husain (a.s), sai Imam Aliyyu Zainul-abidin (a.s), sai Imam Muhammad al'Bakir (a.s), sai Imam Ja'afar asSadik (a.s), sai Imam Musa alKazim (a.s), sai Imam Ali arRidha (a.s), sai Imam Muhammad al'Jawad (a.s), sai Imam Ali al'Hadi (a.s), sai Imam Hasan al'Askari (a.s), sai Imam Muhammad al'Mahadi (a.s).
Hafiz Muhammad Sa'id
hfazah@yahoo.com
www.hikima.org
Thursday, June 16, 2011
 
Sakon Imam Ali (a.s) zuwa ga Malik Ashtar
Nahjul-balaga: Wasika / 53.
[Shi ne mafi tsayin sako da aka rubuta kuma wanda ya fi kowanne tattaro kyawawan sakonni]

Da sunan Allah mai Rahama mai Jin kai
Muhimman abubuwa Hudu ga Jagora (Hadafin Jagoranci)
Wannan shi ne abin da bawan Allah sarkin muminai Ali (a.s) ya umarci Malik dan al'Haris al'Ashtar da shi a sakonsa zuwa gareshi yayin da ya sanya shi shugaban Masar: Hada harajinta, da yakar makiyanta, da gyara mutanenta, da raya kasarta.

Asasin Fikirar Tunani da Ayyukan Jagora
Ya umarce shi da jin tsoron Allah da zabar biyayyarsa, da biyayya ga umarninsa a littafinsa: daga farillansa da sunnoninsa wacce babu wanda zai rabauta sai da biyayyarta, kuma babu wanda zai tabe sai da musanta ta da tozarta ta. Kuma (ya umarce shi da) taimakon Allah matsarkaki da zuciyarsa da hannunsa da harshensa, domin shi Ubangiji (sunansa ya girmama) ya lamunce wa wanda ya taimake shi da taimakonsa, da daukaka wanda ya daukaka shi.

Tsarkakewar Jagora ga Kansa
Kuma ya umarce shi da ya kame kansa gun sha'awowi, ya rike kansa gun burace-burace, domin rai mai umarni ce da mummuna sai dai wanda Allah ya yi wa rahama.
 
Kular jagora ga na kasa da shi
(Yaya kuma ya kamata jagora ya kalli kansa?)
Sannan ka sani ya kai Malik ni na aika ka zuwa gari ne da ya kasance adalci da zalunci sun gudana a karkashin wasu dauloli kafin zuwanka, kuma mutane zasu duba lamarinka kamar yadda kai ma kake duba lamarin masu mulki kafin kai, kuma zasu fadi abin da kake fada kan wadancan a kanka.
Kuma kawai ana gane salihai ne da abin da Allah yake gudanarwa garesu ta harsunan bayinsa, don haka tanadin aiki na gari ya kasance shi ne mafi soyuwar tanadi gunka.
Ka mallaki son ranka, ka hana kanka abin da bai halatta gareka ba, ka sani hana rai shi ne yi mata adalci cikin abin da ta so da wanda ta ki.

Son Jagora ga Jama'arsa
(Wajibi ne son jama'ar kasa dukansu ya kasance shi ne mafi girman siffar jagora)
Ka sanya wa zuciyarka tausayin al'umma da kauna da tausayawa garesu, kada ka zama wani zaki mai cutarwa garesu da ake farautar cinsu, domin ka sani su (jama'a) iri biyu ne, ko dai dan'uwanka a addini, ko kuma tsaranka a halitta, suna samun yin kuskure, kuma cututtuka suna samun su, kuma ana ganin ayyukansu na gangan da na kuskure, sai ka ba su afuwarka da yafewarka kamar yadda (kai ma) kake so Allah ya ba ka afuwarsa da yafewarsa, ka sani kai kana samansu, mai jagorancin lamari duka (shugaban kasa) yana samanka, kuma Allah yana saman wanda yake jagoranka. Kuma tabbas ya wadatar da kai lamarinsu, ya kuma jarrabe ka da su (don ya ga yaya zaka yi adalci ga kanka da kawukansu).
 
Hanin rudar kai ga jagora
(Kuskure ne ga jagora ya ji akwai gaba da fada tsakaninsa da wata jama'ar kasa)
Kada ka sanya kanka mai gaba da yakar Allah, domin babu wani taimako gareka daga azabarsa, kuma ba ka da wata wadatuwa daga afuwarsa da rahamarsa, kada kuma ka yi wata nadama kan wata afuwa, kada ka yi takama da azabtarwa (ga wasu mutane), kuma kada ka yi gaggawar zartar da wani abu (na ukuba) da ka samu mafita (hanyar yafewa) gareshi, kuma kada ka ce ni ma abin umarta ne sai in bi, wannan yana sanya barna a cikin zuciya, kuma shisshigi ne a addini, kuma kusantuwa ne zuwa ga wani (mutum ba Allah ba)!.

Yadda jagora zai yaki son ransa da kawar da rudin kansa
Idan wani abu na takama da jin kai (jin isa) ya sosu a zuciyarka saboda mulkin da kake kansa, to sai ka duba girman mulkin Allah a kanka, da ikonsa kanka da abin da kai ba zaka iya masa ba ga kanka, to wannan zai kwantar da daga kanka, kuma ya kange maka wanda yake iza (zuga) ka, kuma ya dawo maka da abin da ya ragu na hankalinka.

Hana jabberanci da wuce iyaka ga shugaba
Ka yi hattara da daidaita kanka da Allah a cikin girmansa, da kamantuwa da shi a cikin jabarutinsa, hakika Allah yana kaskantar da dukkan jabberi, yana wulakanta dukkan mai takama. Ka yi wa Allah adalci, kuma ka yi wa mutane adalci ga kanka da kuma kebantattun makusantanka, da dukkan wanda kake kauna daga jama'arka, domin idan ba ka yi haka ba, to ka yi zalunci, wanda kuwa ya yi zalunci ga bayin Allah, to Allah zai kasance abokin husumarsa don kariya ga bayinsa, wanda kuwa Allah ya yi husuma da shi to zai kaskantar da madogararsa, kuma shi ya kasance ke nan mai yaki da Allah har sai ya bari ya tuba.
 Kuma babu wani abu da ya fi gaggawar canza ni'imar Allah da gaggauta azabarsa fiye da tsayar da zalunci, domin Allah yana jin addu'ar wadanda aka danne, kuma shi mai yin tarko ne (a madakata) ga azzalumai.

Ma'anar daidato a cikin Siyasar Jagora
(Matsayin jagora gun al'ummar kasa ba gun manyan kasa ba)
Abin da ya fi soyuwa gunka ya kasance shi ne abin da yake mafi tsakaituwa cikin gaskiya (ba shisshigi babu kuma takaitawa), kuma ya kasance shi ne ya fi zama adalci, mafi soyuwa gun al'ummar kasa. (Ka sani) cewa fushin al'umma yana taushe (ya danne) yardar manyan gari, (ta yadda ko manyan gari sun yarda da kai, to ya zama a banza matukar al'umma tana fushi da kai), amma kuma fushin manyan gari to ana shafe shi da yardar al'umma (wato ko manyan gari suna fushi da kai, amma al'umma tana yarda da kai, to wannan shi ne abu mai amfanarka).
Kuma ka sani babu wani mutum a cikin al'umma da ya fi zama (mai dora) nauyi a kan jagora yayin yalwa, kuma ya fi karancin taimaka masa yayin bala'i, ya fi kowa kin adalci, ya fi kowa nacewa da roko, ya fi kowa karancin godiya yayin da aka ba shi kyauta, ya fi kowa karancin bayar da uzuri yayin da aka hana shi, ya fi kowa gajen hakuri yayin da bala'o'in zamani suka fado, fiye da manyan kasa (manyan gari).
(Ka sani) babu wata madogarar addini da hadin kan musulmi, wanda shi ne zaka yi tanadinsa don kariya daga makiya fiye da mutanen gari cikin al'umma, don haka sauraronka ya kasance garesu, karkatarka ta kasance tare da su.

Matsayin jagora gun 'yan leken asiri da masu dadin baki da masu kawo sukan wasu
Mafi nesa da kai daga al'ummarka kuma mafi muninsu a gunka, su kasance su ne wadanda suka fi kowa son tono aibin mutane, ka sani mutane suna da aibobi, shugaba shi ne ya fi cancanta ya rufe su (aibobin).
Kuma kada ka nemi tono abin da ya buya daga gareka, kai aikinka shi ne ka gyara abin da ya bayyana kawai gareka, kuma Allah shi ne mai hukunci kan abin da ya boye maka. Ka rufa asirin (mutane) iyakacin yadda zaka iya, sai Allah ya rufa naka asirin da kake so ka boye shi ga al'ummarka.

Yada nutsuwa da zaman lafiyar al'umma yana daga wajiban da suka hau kan shugaba
Ka kore wa mutane dukkan wani kulli na gaba, ka yanke masu duk wani dalilin juya wa juna fuska, ka kau da kai daga dukkan abin da bai bayyana gareka ba, kuma kada ka gaggauta gaskata duk wani mai kawo maganar wasu, domin duk mai kawo maganar wasu maha'inci ne ko da kuwa ya shiga rigar masu nasiha.
Ka da ka shigar da marowaci cikin shawararka da zai hana ka yin alheri yana mai nuna maka (zaka) talauta, ko wani matosaraci da zai kawo maka rauni daga lamurranka, ko mai kwadayi da zai kawata maka zari (handuma da babakere) da danniya, ka sani rowa da tsoro da kwadayi dabi'u ne mabambanta, munana zato ga Allah shi ne asasinsu.
 
Zabar Wazirai (mataimaka) da sake su
(Siffofin wazirai kyawawa da munana)
Lallai mafi munin waziranka su ne wadanda suka kasance wazirai ga ashararan jagorori da wadanda suka yi tarayya da su cikin sabon Allah kafinka! Kada ka bari su zama abokan sirrinka, ka sani su mataimakan masu sabo ne, 'yan'uwan azzalumai. Kuma zaka iya samun wasu mutanen da suka fi su wadanda suke da ra'ayoyi da matsayi kuma ba su da irin laifuffukansu da zunubansu daga wadanda ba su taimaki azzalumi a kan zaluncinsa ba, ko wani mai sabo a kan yin sabonsa ba.
Wadannan su ne suka fi karancin dora maka nauyin (bakin jini), kuma suka fi kyautata maka taimako, suka fi tausayawa gareka, suka fi karancin samun sabo da wani ba kai ba. To sai dauke su a matsayin na kusa da kai domin kebewarka da shiga taronka, sannan kada ya zama wanda ya fi kowa a gunka, shi ne wanda ya fi gaya maka gaskiya mai daci, ya fi karancin ba ka taimako kan abin da kake yi wanda Allah yake kin sa ga masoyansa, komai kuwa son da kake wa wannan (sabon).



1 2 3 4 next