Halayen Manzon Allah (s.a.w)



Ba kawai manzon Allah (s.a.w) hatta da Imam khomain wanda bai kai darajar kurar da manzon Allah (s.a.w) ya taka ba, amma sai ga shi Fedal Kasto na Cuba da ya ga gidan da yake rayuwa yana cewa: "Idan dai kwaminisanci yana nufin mu rayu iri daya da babu bambanci tsakanin talaka da jagora to lallai Imam Khomain ya fi mu kwaminisanci", wannan ga malamin gaskiya mai imani da tsoron Allah da yake kokarin ya kwantanta rayuwar manzon Allah (s.a.w) ke nan, ina ga a ce Fedal Kasto ya ga annabin ne kansa.

Sannan kuma yana ci da bakonsa wannan ma wani abu ne mai muhimmanci wanda ya kamata duniya ta yi rubuce rubuce a kansa, domin mafificin al'ummar duniya amma yana ci da baki, kuma yawancinsu mun san mutane ne da suke zo masa daga kauyuka. Don haka mai ji da sarauta ko takamar yana da dukiya ko matsayi ya duba matsayin gaskiya na mafificin halitta, ya yi koyi da shi, ya sauke rawanin tsiya da ya sanya a kansa, domin samun mafi tsira a lahira, da soyayyar Allah madaukaki da bayinsa a duniya.

Manzon Allah (s.a.w) ya kasance yana tuna Allah (s.w.t) a kowane abu, don haka zamu ga idan aka ajiye abinci a gabansa sai ya ambaci sunan Ubangiji madaukaki, idan kuwa ya gama sai ya gode masa, kuma bai taba gafala ba ko sau daya ko mantuwa da yin hakan, hatta da sahur da shan ruwa.

 

 

Idan kuwa zai ci abinci sai ya zauna kamar yadda bayi suke zama don kaskan da kai ga Allah (s.w.t), kuma ya zauna da nutsuwa sai ya ambaci Allah (s.w.t), sannan sai ya ci da 'yan yatsu uku ko hudu ko da tafinsa, kuma yana cin gabansa ne ba ya bin gaban wasu, sannan idan shi ne ya zo da abicin sai ya fara.

A kowane abu manzon Allah (s.a.w) yana kiyaye hakkin mutane, don haka ne ya kasance ba ya cin tafarnuwa ko albasa, ko wani abu da yake da warin da mutane suke cutuwa idan sun shake shi. Sai dai duk da haka ba ya kushe abin da ba ya cin sa, idan ya kayatar da shi sai ya ci, idan kuwa abin ci bai kayatar da shi ba sai ya bari ba tare da ya kushe shi ba.

Idan ya gama cin abinci sai ya sude hannunsa, sannan sai ya tsarkake ta da wani kyalle, sannan sai ya wanke hannun, ya shafe shi da wani kyalle, don haka ne ba a samun hannunsa yana kanshin abin da ya ci.

 Sannan ba ya ci shi kadai sai ya samo mai taya shi, yana ganin mafi sharrin mutane shi ne wanda ya ci shi kadai, ya daki bawansa, ya hana mutane abincinsa. Kuma ba ya cin mai zafi yana yana umarni da a bari sai ya yi sanya, yana ganin shedan yana da rabo a abinci mai zafi.

Sannan akwai abin ci masu yawa da ruwayoyi suka kawo cewa manzon Allah (s.a.w) yana cin su da suka hada da dabino, da sukari, da gishiri, da alkama, da duma, da kankana, da gishiri, da kayan marmari, da inabi, da gurasa, da nono tare da dabino. Haka nan yana cin nama gasasshe, yana ganin yana da amfnai wurin karfafa ji da gani, yana cin naman kaji, da tsuntsaye, yana son karfata daga tumaki da awaki. Kuma yana cin gurasa da mai, yana shan kunu, yana cin abubuwan da suke a kasa kamar irinsu dankali da makani.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 next