Kimar Mutum



Sannan akwai abin mamaki ga wannan halitta ta mutum mai sirri maras iyaka, sai dai Allah madaukaki ya yi mana bayani ta hannun annabawansa da wasiyyansu ka n dalilin da ya sanya shi halittar wannan halitta mai ban mamaki.

Ubangiji madaukaki yana cewa: Ban halicci mutun da aljani ba sai don su bauta mini. (Zariyat: 56).

Imam Ali (a.s) ya ce: "An umarce ku da tsoron Allah ne, kuma an halicce ku don kyautatawa da biyayya ne". (Nahajul balaga: Ibn Abil hadid/3/108)

Imam Husain (a.s) ya ce: "Ya ku mutane, Allah mai daukakar ambato bai halicci mutane ba sai don su san shi, idan suka san shi sai su bauta masa, idan suka bauta masa sai su wadatu daga bautar waninsa. Sai wani mutum ya ce: Ya dan manzon Allah (s.a.w), ina fansarka da iyayena, mene ne sanin Allah? Sai ya ce: Sanin kowane mutanen zamani Imaminsu wanda yake wajibi ne su yi masa biyayya". (Biharul Anwar: 23/83/22).

Imam Sadik (a.s) yana cewa: -yayin da wani zindiki ya tambaye shi cewa; saboda me Allah ya halicci halitta alhalin ba ya bukatar su, kuma babu wanda ya tilasta masa kan halitta su, kuma ba ya cancanta ya yi wasa da mu?- "sai Imam (a.s) ya ce: Ya halicce su domin su yi abin da zasu samu rahamar Allah da shi ne, sai ya yi musu rahama". (Biharul Anwar: 10/167/2).

Magana kan wannan lamari tana bukatar rubutu na musamman don haka sai mu kulle ta hakan, sai dai duk da hakan mutum yana da wani rauni maras misali. Duba abin da mahaliccinsa yake cewa: “An halicci mutum mai rauni”. (Nisa'i: 28).

Sannan wasiyyin manzon rahama Muhammad (s.a.w), Imam Ali (a.s) yana cewa: Mutum miskini ne; Ajalinsa boyayye ne, ciwuwwukansa taskace suke, aikinsa kiyayye ne, sauro yana sanya shi zogi, shakewa (kwarewa) tana kashe shi, dan gumi yana sanya shi wari. (Nahajul balaga: Ibn Abil hadid /20/62).

Wannan ruwaya tana nuna mana matukar raunin mutum a cikin samammun bayin da Allah madaukaki ya halitta.

Ya kai dan Adam ka koma ka san matsayinka gun ubangijinka, ka san jagoran zamaninka, domin ka samu tsira gun Allah (s.w.t) daga dukkan kaskanta, ka kuma samu kamalar da ba ta da iyaka a wurinsa!.

Cibiyar Al’adun Musulunci

www.hikima.org

Hafiz Muhammad Sa’id

hfazah@yahoo.com

Wednesday, April 07, 2010



back 1 2 3 4