Musulmin Duniya



Mu koma wa tarinin musulunci mu ga sakon Annabi (s.a.w) da ya bayar da kariya ga dukkan masu addinan sama, sai bayahude da kirista suka zauna a cikin daular musulunci a cikin mafificin aminci da babu kamarsa a tarihi, ba mu taba ganin musulunci ya taba wani ba sai wanda ya taba shi.

Kuma sau da yawa mun ga hakurin musulmi duk da suna da karfi da iko amma sai masu wani addini ya yi musu isgili su jure, mu duba imam Bakir (a.s) jikan Manzon Allah (s.a.w) da isgilin da wani kirista ya yi masa. Imam Muhammad Bakir (a.s) ya kasance ma'abocin fifiko, da daukaka, da addini, da ilimi mai yawa, da hakuri mai yalwa, da kyawawan halaye, da ibada, da kaskan da kai, da baiwa, da rangwame.

Ya kai karshen kyawawan dabi'u wani Kirista ya ce masa: Kai bakar ne. (wato; saniya), Sai ya ce: Ni dai Bakir (Mai tsage ilimi) ne. Sai Kirista ya ce: Kai dan mai dafa abinci ne. Sai ya ce: Wannan aikinta kenan. Sai Kirista ya ce: Kai dan bakar mace ne ballagaza. Sai ya ce: Idan ka yi gaskiya Allah ya gafarta mata, idan ka yi karya kuma Allah ya gafarta maka. Sai wannan Kirista ya musulunta!

Muna iya ganin yadda wannan mutumin ya kai matukar keta hurumi da cin mutuncin Uwa ta wannan Imami mai girma amma sai ya jure ya yi irin halin kakansa, sai ga shi sakamakon haka wannan Kiristan ya musulunta!.

Kissoshin Annabi (s.a.w) da wulakancin da wadanda ba musulmi ba suka yi masa, da juriyar da ya yi suna da yawa, kuma sun nuna mene ne musulunci, kuma da yawa sun musulunta saboda haka. Kada mu manta fa a wannan lokacin da yake jure wannan wulakancin shi ne shugaban daular musulunci, amma sai ya jure domin ya kasance rahama ga talikai, haka nan wasiyyansa suka yi irin wannan juriya tasa suka kasance rahama ga talikai. Don me mu ba zamu samu yin kyakkyawan koyi da shi ba, don me mu ba zamu nuna wa duniya hakikanin musulunci ba!

Wani Kiristan arewacin Nijeriya (ta tsakiya) yana jin an zalunce shi a tarihin rayuwarsa, kuma yana jin musulunci ne ya yi masa, don me musulmi ba zasu wayar da kansa ba ya gane cewa babu wani musulunci da ya zalunce shi. Ya san cewa idan an zalunci ne da sunan musulunci to lallai an zalunci musulunci ne kawai. Kuma ya gane cewa ba shi kawai aka zalunta a tarihi ba, musulmi ma an yi masa wannan zaluncin. Idan kuwa ba a zalunce shi ba to don me yake ganin an yi masa zalunci a tarihi!? Idan kuwa an zalunce shi ne, to yana nufin shi kuma abin da yake yi yau kan musulmi yaya sunansa!?

Mu zauna a teburi daya da mai matsala da mu, mu san meye matsalar, idan muka ga muna da kuskure sai mu ba shi hakuri mu nemi yafewa, sannan sai mu kulla zumunci da shi; A bayanin Malam Kira'ati; ranar alhamis 17, ga Rabi'ul Awwal, 1431, yana raddi ga masu sukan daular musulunci yana cewa: "Idan ka ce: Akwai aibi a daula haka ne, kuma neman cewa babu wannan aibin kuskure ne, amma cewa ta rushe saboda akwai aibi laifi ne babba mai girman gaske. Babban abin nuni da shi a nan cewa mai aibi bai kamata ya yi musun aibin ba, amma shi kuma mai cewa; akwai aibi ba yana nufin ya rusa abin da yake gani da aibi ba, sai dai ya nemi gyara.

Musulunci ya yi furuci da cewa kirista da bayahude suna da addini, sai dai a yi bahasi da su da hikima da kyautatawa domin dauke rashin fahimta da suke ciki, ya kira su da zama tebure daya domin karfafa juna da bin abin da suka yi tarayya a ciki, da tattaunawa cikin hikima a inda suka yi sabani yana mai cewa: "Ka ce: Ya ku ma'abota littafi ku zo zuwa ga kalma madaidaiciya a tsakaninmu da ku…" (Aali Imrana: 64). Da fadinsa: "Kada ku yi jayayya da ma'abota littafi sai da wacce take ita ce mafi kyau…" (Ankabut: 46).

Kamar yadda ayoyi masu yawa suka zo suna masu karfafa imanin musulmi da dukkan annabawan Allah da dukkan littattafansu. Kuma tarihi ya nuna yadda musulunci ya girmama dukkan addinai saukakku ya mutunta musu tunaninsu. Sai dai an samu rashin fahimta tsakaninsu a tarihi wanda jahiltar juna ya haifar da shi, kuma wannan bala'in a yanzu haka ya fi da kamari. Ba komai ya haifar da yakin 'yan mishan a kan daulolin musulmi ba shekaru 500 da suka gabata sai wannan rashin fahimtar juna. Kuma wannan ya samo asali ne daga kauce wa koyarwar wadannan ayoyin da suke sama.

Sannan mafi girman takaitawa tana gunmu da muke da wannan tsarin saukakke daga Allah da ba mu isar da shi ba yadda ya dace, sai aka wayi gari mu mun ki tsayawa mu fahimci sakon da kyau saboda mun dauka kamar gado yake, balle wadanda ba musulmi ba da su ma ba su san sakon ba. Sai dai har yanzu ba mu yi lati ba, masu hankali da ilimi daga cikinmu ya kamata su karanci abin su san inda zasu fara domin isar da sakon rahamar ga dukkan talikai.



back 1 2 3 4 5 next