Ladubban Soyayya



D- Rowa

219. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Babu alheri ga aboki marowaci[19].

220. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Rowa tana kawo gaba da kiyayya[20].

221. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Rowa tana kaskantar da mai yenta, kuma mai nisantarta yana daukaka[21].

E- Sakin Jiki

222. Daga Imam Ja’afar Sadik (A.S) ya ce: Kada ka amincewa abokinka gaba daya, ka sani kayen nan na sakin jiki ba a iya mayar da hasararsa[22].

F- Cutarwa

223. Kanzul Ummal; daga Anas: Daga Manzon Allah (S.A.W) ya kasance idan ya tsaya da dare yana karatu, sai ya yi sauti da murya kadan a cikin karatunsa, sai aka yi masa magana game da hakan, aka ce masa: me ya sa ba ka dada sautinka a karatu? sai ya ce: Ina kin in cutar da wani abokina da ahlin gidana[23].

G- Wulakanci

224. Daga Manzon Allah (S.A.W) ya ce: ku kasance bayin Allah kuna ‘yan’uwa, musulmi dan’uwan muslumi ne, kada ya zalunce shi, kada ya tabar da shi, kuma kada ya wulakanta shi[24].

H- Wuce Gona Da Iri A Kauna

225. Daga Manzon Allah (S.A.W) ya ce: ka so masoyanka da sauki haka nan, ta yiwu ya kasance makiyinka a wata rana haka nan, ka ki makiyinka da sauki haka nan, tayiwu ya kasance masoyinka wata rana haka nan[25].

226. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Daga Manzon Allah (S.A.W) ya ce: kada sonka ya kasance kallafa wa kai, kuma kada kin ka ya kasance a banza; ka so masoyinka da sauki haka nan, kuma ka ki makiyinka da sauki haka nan[26].

I- Sabo Saboda Aboki

227. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: mumini ba ya zaluntar wanda yake ki, kuma ba ya daukar alhaki domin wanda yake so[27].

J- Yada Duk Wani Sirri

228. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: ka ba wa abokinka dukkan soyayya, kada ba shi dukkan nutsuwa, ka ba shi dukkan taimako, kada ka ba shi dukkan asirai; (da haka ne) zaka ba wa hikima hakkinta, kuma ka yi wa abokinka abin da yake wajibi ne a kanka[28].



back 1 2 3 4 5 6 7 next