Ladubban Soyayya



E- Cudedeniya

210. Daga Imam Ridha (A.S): yayin da aka tambaye shi mene ne hankali: juriya kan bakin ciki, da kuma raha ga makiya, da kuma cudanyar abokai[10].

6 / 2

Abin da bai kamata ba a zamantakewar ‘yan’uwa

A- Batar Da Kama

211. Daga Manzon Allah (S.A.W) ya ce: uku Allah ba ya kallon su ranar alkiyama kuma ba ya tsarkake su kuma suna da azaba mai radadi: mai jan wandonsa kasa saboda girman kai, da mai yabon kayan sayarwarsa da karya, da kuma mutumin da ya fuskance ka da so da kauna a zuciyarsa amma sai ya wuce ya kule (ya bace daga gani), zuciyarsa tana cike da algush[11].

212. Daga Manzon Allah (S.A.W) ya ce: idan ilimi ya bayyana, aka tsare aiki, kuma aka hadu a harsuna, aka saba a zukata, aka yanke zumunci, to a nan ne “Allah ya la’ance su kuma ya kurumtar da su, kuma ya makantar da ganinsu”[12].

213. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Da yawa mai kauna ya zama na karya ne[13].

B- Mummunan Zato

214. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Kada zato ya bata maka wani aboki da yakini ya gyara maka shi[14].

215. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Kada mummunan zato ya yawaita gareka; domin ba zai bar maka wani sulhu ba tsakaninka da wani masoyi[15].

C- Algush

216. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: algus din aboki, da yaudarar alkawura, suna daga ha’incin alkawari[16].

217. Daga Imam Ja’afar Sadik (A.S) ya ce: kada ka yi wa mutane algush sai ka wanzu ba ka da wani aboki[17].

218. Daga Imam Ja’afar Sadik (A.S) ya ce: kada wani mai girman kai ya yi tsammanin yabo kyakkyawa, haka nan kada mayaudari ya yi tsammanin samun yawan abokai[18].



back 1 2 3 4 5 6 7 next