Mene ne Auren Mutu'a



Ma'ana:

"Kuma da Mata masu aure banda abinda hannuwan ku suka mallaka (Baiwa)"

Malam Ibn Kathir ya fada a cikin littafinsa na Tafsiri cewa ita wannnan "Illaa maa malakat aimaanikum" ana nufin banda abinda hannuwanku suka mallaka na Fursunonin Yaki, domin kuwa su halas ne gareku, kuyi Jima'i da su yayin da sukayi Istibra'i, (yace) hakika wannan Aya ta sauka ne akan haka. Sannan yace: Malam Ahmad Hanbali (cikin littafinsa) 2/72, yace: "Munzo da Fursunonin Yaki daga Fursunonin Yakin ranar "Audas" a cikin su akwai Mata. Sai muka ki muyi tambaya akansu, akwai Mata a cikin su. Sai Annabi (Sallallahu alaiHi wa Alihi) ya tambaye mu, a take sai wannan Ayar ta sauka, aka halasta mana Farjinsu (Tafsirin Ibn Kathir: juzu'i na 1, shafi na 474).

Sannan Malam Muslim ya fitar ta hanyar Sa'idu dan Abii Urwata daga Katadata daga Abil-Khalil Alkamatul-Hashimiy daga Abi Sa'idul-Khudriy, Hakika Manzon Allah (Sallallahu alaiHi wa Alihi) ya tura Runduna zuwa "Audas" ranar Hunainu suka riski Makiya inda suka cimmasu, sukayi galaba akansu, suka kamo Fursunonin Yaki. Sai mutane daga Sahabban Manzon Allah (Sallallahu alaiHi wa Alihi) suka zamanto abin gwasale daga masu ziyartarsu a dalilin matansu, daga ciki akwai Mushrikai. Sai Allah Ta'ala ya saukar da "Wal-muhsanatu ……" ai su halasne gareku idan sun gama Idda. (Al-Aja'ib fii bayanil-Asbab: juz'i na 2, shafi na 855).

Da wadannan takaitattun Hadisai zamu fahimci cewar akwai wata alaka da Addinin Musulunci ya yarda da ita, wacce ta halastawa Namiji Saduwa da Mace, wato hanyar mallakar Baiwa. Babu wani batun daura aure sai dai kawai ka jefa ta Daki abinka. Don hakane ma ta samo suna a Hausance da (Sadaka),wato ka saka a Daki. Sannan wani abin a kula game da Sadaka ko Kwarkwara (Baiwa) shine, babu wani maganar Saki fa illa yayin da ka siyar ko ka bayar da ita (Baiwar) shine Sakinta. To kaga ashe Ala gafarta Mallam bawai ta hanyar Daura aure ne kadai Mace ke halasta ga Namiji ya Sadu da Ita ba.

In dai har kana kyamar Mutu'a don rashin bayyana Daurin aure a fili ne, to ya zaka ce kuma akan Kwarkwara da itama ba a bayyana Daurin auren ta bilhasali ma ita Kwarkwara babu wani Daura aure kwata-kwata a wajen mallaka?! Ko kuwa kana kyamar tane don babu Saki a cikinta? To idan haka ne yaya zaka ce kenan akan Kwarkwara da itama babu Saki a wajen rabuwa da Ita? Sakin ta shine ka sayar ko bayar da ita shike nan alaka ta kare. Idan kuwa tunanin ka ya tafi ne wajen rashin Wajabta Ciyarwa, Shayarwa, Dawwamammen Matsuguni, to yaya zaka ce akan auren Da'imi da shima wadannan hakkokin kan saraya yayin da Matar ta zamo Ballagaza marar kama kai, kuma auren ya cigaba a hakan? Shin zaka iya kace zaman da Shari'a bata yarda da shi bane shima?!

Kwarkwara wacce Hausawa kan kira da "Sadaka" nasan ba zakayi inkarin cewa har yanzu anan Kasar da wasu tsirari ana riko da Ita ba. Halascin Kwarkwara ya faro ne tun daga zamanin Fiyayyen Halittu Annabi Muhammadu (Sallallahu alaiHi wa Alihi), kamar yadda bayanin hakan ya gabata daga Hadisan Annabin da ya fito ta hanyar Abu Sa'idul-Khudriy. Wanda sun nuna cewa ita Kwarkwara ana samun tane daga Ganimar Yaki, wanda akayi shi tsakanin Musulmai da Kafirai. Ko kuma kai ka siya daga

To abin tambaya anan shine:  shin har yanzu ana Yaki tsakanin Musulmai da Kafirai ne da za'ace an sami Ganimarsu?! Ko kuwa su 'Yayayen wadancan ne abin yake gangarowa har kawo i yanzu?! Ko kuwa shima dan da Ubangijin Baiwa ya Haifa shima ba da ba ne Bawa ne?! Don dai ni nasan ko Yakin Shehu Usman dan Fodiyo babu Ganima a cikinsa, don kuwa Yaki ne tsakanin Musulmai da Musulmai (Muminai da Azzalumai). Shi kuwa ba a rikarwa duk wanda yayi Shahada guda biyu (wanda yayi Imani da Ubangiji da Manzon sa) Dukiya, Mata, da sauran su a matsayin Ganima. Duba cikin Tarihin da zai zo nan gaba, Halifa na biyu ne yake yiwa Halifa na daya hani daga Manzon tsira (Sallallahu alaiHi wa Alihi) akan Yakar wadanda basa bashi Zakka. Saboda yana ganin sun Shaida da Shahada biyu.

Don haka Yakin Shehu Usman ma tsakanin Muminai ne da Azzalumai, shi yasa aka kirawo shi da TAJDIDI. Wato Jaddada Musulunci. A Kasar Sa'udiyya yau kusan Shekaru Dari da motsi kenan da hana cinikin Bayi tunda Aali Sa'ud suka karbi Mulki daga hannun Turkawa wadanda da Kasar a hannun su take. Wanda shi kansa wannan cinikin Bayin tun na wancan lokacin gurbatacce ne a Addinin Musulunci. Don kuwa ya ginu ne akan zalunci, dukkansu Musulmi ne, amma sai suke Bautar da Ajnabi (mutumin da ya shiga Kasar Bako musamman ma Bakar fata). Kuma su kansu basu hanu ba sai da Sarkin ya rika bin duk wanda ke da Bawa yana yanka shi. Wannan ne ma yasa idan kace da Dan Sa'udiyya "Dajaj Sa'ud" wato Kajin Sa'ud, (Sa'ud din Sarkin Makka ne na wancan lokacin), to sai dai Shari'a ta raba ku dashi. Domin kuwa haka ya rika bin Kakanninsu yana yankawa kamar Kajin, saboda sunki su daina bautar da Mutane. To ina ga kuma

To abin lura anan nasan dai mai Karatu kasan cewa: Mai Martaba Wane, da Mai Girma Wane, da Shehi Wane, da Malam Wane, da Alhaji Wane, dukkansu suna da Kwarkwarori! Ga Wane da Wane nan duk ka sansu tare kuka taso tun kuna Yara 'Yayan Kwarkwarori ne. Abin tambaya anan ta yaya aka samo su wadannan Kwarkwarorin a irin wannan lokacin wanda tsawon lokaci ya yanke daga samun halastattun Bayi irin wadanda Addinin Musulunci ya yarda da su musamman ma mu a wannan Nahiya? Bazai taba yiwuwa ace Shehi Wane a irin girmansa, da Mai Martaba Wane a irin martabarsa da Alhaji Wane basu san haka bane. To idan kuwa sun sani yaya matsayin 'Yayayen nasu? To la budda akwai wani boyayyen sirri a bayan



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 next