Mene ne Auren Mutu'a



 

index

next

Mene ne Auren Mutu'a

Bismillahir Rahmanir Rahim

Alhamdu lillahi Rabbil Alamin, wa afdhalus salati wa atammut taslim ala Khatamil Anbiya'i wal Mursalina Muhammadul Musdafa wa Alihid Dahirinal Mujtabin, allazina azhabal Lahu anhumur rijsa wa dahharahum tadhira.

Lokuta da daman gaske nakan rasa gane menene kan fusata mutum har yayi munanan lafazai yayin da yaji an furta kalmar "Mutu'a". To amma da na dan yi dogon tunani sai naga ashe ba sasakai ba, babu makawa a bayan wannan kalmar akwai wani boyayyen abu, ba wai kalmar bace kadai. Domin kuwa da na yi tunani kan wadannan kalmomi na JAKI DA ZAKI, akan menene ke fusata mutum yayin da aka kira shi da Jaki, kuma menene ke dadada masa yayin da aka kira shi da Zaki? Sai mu ga ashe a dai-dai lokacin mutum kan hararo wata halitta ne mai dauke da wannan Suna. Don haka a lokacin ba yana kallon Sunan bane a matsayin wasu harafai guda hudu (J-A-K-I, Z-A-K-I) a'a yana kallon wannan sunane a matsayin Siffar Dabba mummuna ko kuwa kyakkyawa.

To idan hakane me ke faruwa ga kalmar "Mutu'a" da har idan mutm yaji an ambace ta kan fusata har yayi mummunan furuci? Shin irin abinda yake faruwa ne akan kalmar Jaki ko Zaki? Don haka ashe lokacin da kalmar Mutu'a take tsirgawa cikin Kunnen mai sauraro ba komai Zuciyar sa ke kawo masa ba illa ga wasu mutane guda biyu Namiji da Mace a kwance cikin aikata wata alaka da shi a tunanin sa, aure ne kadai kan shiga tsakaninsu har Addinin Musulunci ya amince da wannan alaka tasu. saboda haka kasantuwar wannan yasa yake kallon "Mutu'a" da wani irin kallo na daban.

Shin aure ne kadai kan sa Musulunci ya amince da wata alaka ta Jima'i tsakanin Namiji da Mace?! Amsa a'a! Ba lalle sai da aure a tsakanin ka da Mace zaka iya hulda da Ita har kuyi Jima'i ba. Idan muka duba cikin littafin Allah mai tsarki zamu samu Allah Madaukakin Sarki yana cewa:

"وَاْلمُحْصَنَاتُ مِنَ اْلنِّسَاءِ إِلاَّ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانِكُمْ........"



1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 next