Nuna Kauna Ga Mutane



Kamar yadda aka ruwaito da ingantaccen isnadi daga wajen Abi Abdillah (a.s) yana cewa: “Lalle cikan gaisuwa wajen mazaunin gida ita ce musafaha, sannan cikan gaisuwa ga matafiyi ita ce runguma[26]”.

Ba WaMutum Labarin Kaunar da Kake Masa

Na uku: labarin da mumini zai bai wa dan’uwansa mumini kan irin kaunar da yake masa, a wasu lokuta bayyanar da hakan ya kan kasance ne ta hanyar aiki, kamar musafaha, runguma da sumbanta kamar yadda ya gabata, a wasu lokutan kuma ya kan kasance ne ta harshen baki (magana) da ba shi labarin hakan. An ruwaito daga Abi Abdillah (a.s) da take nuni da hakan, inda yake cewa: “Idan kana son mutum ka sanar da shi hakan, don hakan ya kan tabbatar da soyayya a tsakaninku”, a cikin wata ruwayar kuma ta daban “saboda hakan na dawwamar da soyayya da shakuwa”, a cikin na uku kuma cewa ya ke yi “Idan ka so wani daga cikin ‘yan’uwanka, to ka sanar da shi hakan, saboda (Annabi) Ibrahim (a.s) cewa ya yi: “Ya Ubangijina! Ka nuna mini yadda Kake rayar da matattu. Ya ce: shin, kuma ba ka yi imani ba ne? Ya ce: Na’am, kuma amma domin zuciyata, ta natsu[27]”.


[1] . Wasa’il al-Shi’a 8:510, babi na 106, hadisi na 1.

[2] . Al-Kafi 2:234, hadisi na 14.

[3] . Al-Kafi 2:103, hadisi na 5.

[4] . Wasa’il al-Shi’a 8:512, hadisi na 2.

[5] . Wasa’il al-Shi’a 8:512, hadisi na 4.

[6] . Wasa’il al-Shi’a 8:248, hadisi na 3.

[7] . Wasa’il al-Shi’a 8:552, hadisi na 1.

[8] . Wasa’il al-Shi’a 8:494, hadisi na 2.



back 1 2 3 4 5 6 7 next