Halayen Manzon Allah (s.a.w)



Wannan lamarin ne ya sanya hatta da samari ana raba musu kayan shaye-shaye kuma a raba musu makamai domin su kashe junansu, kuma a nesanta su daga ilimi da hankali, don haka ne ake ba su kayan maye. Yayin da shi mai ba su din ba zai yarda ba daya daga cikin kannensa su shiga wannan aikin balle 'ya'yansa kuma, amma ya dauki al'ummarsa abin gwaji domin cimma nasa hadafi ba nasu hadafin ba.

Balle kuma su samu matsayin da zasu je su zauna da shi domin su ci abinci a teburi daya, su gaya masa matsalolinsu, ya share masu hawayensu. Amma sai ga wanda duk wani abu da aka halitta yana kasan darajarsa, wanda shi ne ya samu feshin ilimin Allah na farko da kuma siffofinsa madaukaka, sai ya kasance mai rahama da jin kai, sai ga shi yana zama da wadanda suka zo wurinsa suna cin abinci tare.

Yana ci tare da wadanda suka zo wurinsa na daga musulmi, kuma a kan kasa, wannan halayen na fiyayyen halitta da an samu shugabannin duniya sun kwatanta kashi 10% na wannan halaye masu daraja da an samu ci gaban dan Adam. A kasarmu akwai shahararren malami guda miloniya ne domin yana da kudi da gidaje da ba sa kirguwa, amma babu wani wanda zai ce ya taba zuwa gidansa ya samu wani abin sha koda kuwa ruwa ne balle kuma abinci.

Kai tir da masu sanya rigar sunan musulunci balle malanta amma suna da dabi'un da ko fir'auna ya fi kyautatawa ga mabiyansa. Ba komai ya sanya ni fadin haka ba sai domin fir'auna yana jiyar da mai biyayya gareshi na daga kabilarsa ta kibdawa dadi, yana kaskantar da wasu kabilu ne na Banu Isra'il da yake ganin sun zo bakin haure sun mamaye musu wuri wadanda a ganinsa sun zo sun bata masu addini da gargarjiya ne tun lokacin annabi Yusuf (a.s).

Kuma ayar Kur'ani mai daraja ta yi nuni da wani lamari mai muhimmanci yayin da ta yi wa wasu daga sahabban annabi (s.a.w) fadar cewa idan sun ci abinci a gidansa sai su fita, ba sai ya yi musu nuni ba da cewa su fita. Wato manzon Allah (s.a.w) mai tsananin kawaici da kunya ba ya iya gaya musu cewa idan an ci abinci a fita daga gidansa, sai da ubangiji mai tsananin kishi gareshi ya yi musu fada da abin da suke yi bai dace ba.

Sannan kaskan da kansa ya sanya shi ci a kasa, ba tare da kallon kansa da matsayinsa wurin Allah ba, sai ya kalli kansa a matsayin cewa shi daga kasa yake, kuma cikinta zai koma bayan mutuwarsa, don haka sai ya kasance mai daukakar kaskan da kai, bai kalli turbayar sama ba wacce tasa ta bambanta da ta sauran sahabbansa wanda da ya ga dama da ya yi hakan, amma sai ya kalli turbayar kasa domin ya daidaita kansa da sauran, sai ya bar musu darasi yayin da zasu kasance shugabanin al'umma bayan wucewarsa.

Sai ya ci abin da suke ci, kuma ya sha abin da suke sha, bai ware nasa kwanon daban ba a matsayin kwanon annabi, ko cokalin annabi, ko kofin shan ruwan annabi. Sai ya yarda ya yi tarayya da sauran kan dukkan abin da yake amfani da shi, kamar yadda ya yarda ya ci daga dukkan abin da suke ci.

Bai yarda da ware wani nau'in abinci mai maiko a matsayin nasa daban ba, kuma wannan mummunar dabi'ar da annabi ya yaka mun same ta hatta tsakanin masu da'awar su ne masu kishin addini a duniya, sai a ware wa shugaban wani abinci da talakan da ake tare da shi ba zai iya cin sa ba.

Lallai baban Kasim (s.a.w) duk wanda ya yi da'awar yana kan halayenka daga mutanen duniya da suke raye in banda halifanka na goma sha biyu Imam Mahadi (a.s), ko waye kuwa to wallahi ya yi karya, wanda duk ya yi da'awar ya kiyaye sunnarka kamar yadda kake ya yi jafa'i ga Allah mahalicci kuma ya yi isgili da dukkan kyawawan halaye.

Ba kawai manzon Allah (s.a.w) hatta da Imam khomain wanda bai kai darajar kurar da manzon Allah (s.a.w) ya taka ba, amma sai ga shi Fedal Kasto na Cuba da ya ga gidan da yake rayuwa yana cewa: "Idan dai kwaminisanci yana nufin mu rayu iri daya da babu bambanci tsakanin talaka da jagora to lallai Imam Khomain ya fi mu kwaminisanci", wannan ga malamin gaskiya mai imani da tsoron Allah da yake kokarin ya kwantanta rayuwar manzon Allah (s.a.w) ke nan, ina ga a ce Fedal Kasto ya ga annabin ne kansa.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 next