Isma Kyauta Ce



Don haka wani lokaci; kokarin da mutum yake yi nasa na kansa, da kuma al'ummar da ya taso, da yanayinta yana daga cikin abubuwan da suke haifar da salihancin bawa da kamalarsa. Idan Annabi (a.s) ko wani wasiyyin Annabi (a.s) ya yi kokari, ya samu kamalar da ta cancanta a samu wannan baiwa ta Allah (s.w.t), ya yaki ransa mai neman yin sabo, to babu wani abu da zai hana Allah ya yi masa wannan baiwa mai daraja.

Misalin Yusuf (a.s) da kissarsa da Zulaiha babban misali ne a nan; Yusuf: 23. Haka nan ma misalin gudun da Annabi Musa (a.s) ya yi daga mutanensa; Surar Kasas: 23-24, 15-20. Kuma akwai misalai masu yawa da suke nuni ga rayuwar samartakar annabawa (a.s) da kokarinsu tun suna kanana har zuwa girmansu. Wadannan abubuwan da wasu suna samuwa ta hanyar halitta, wasu kuwa ta hanyar zabin dan Adam duk suna taimakawa wurin samun wannan falalar ubangiji mai girma. Don haka idan Allah ya duba zukatan bayinsa da kokarinsu sai ya zabi mafifitansu ya yi musu ludufinsa a cikin bayinsa, ya kuma ba su aiki mai girma na isar da sakonsa, da kasancewarsu ma'auni na shiriyar dan Adam a cikin bayinsa.

 

Amma batun mai cewa: Idan dai isma ta kasance tana hana zababbun bayi yin sabo a matsayinta na kyautar Allah, to ashe ke nan ba zasu iya sabo ba koda kuwa sun so, kuma ke nan ba su cancanci yabo ko lada ba, don sun bar sabo?

Muna iya cewa; Isma ba ta cire musu zabi, kuma duk sa'adda suka so suna iya sabawa, kamar dai hankali ne da Allah ya yi wa bayinsa ludufi da shi, wanda suna iya sanin mummuna da kyakkyawa da shi. Masu hankula sun san cewa zalunci yana da daci, da zafi, kuma ba sa son a yi musu zalunci, amma kuma sai su zalunci wani, suna iya sanin cewa wani abu zai kai su ga cutuwa amma kuma su aikata shi, wannan kuwa yana nuni da cewa wannan ilimi da suke da shi bai hana su zabin kansu ba.

Haka nan ma lamarin annabawa (a.s) ilimin da aka ba su ba ya hana su zabin kansu, kuma ba ya cire musu ikon sabawa, sai dai su suna kokarin ganin ba su saba ba fiye da kowane mutum, kuma Allah madaukaki ya san haka garesu, don haka sai ya zabe su da wannan falalar tasa. Muna iya kawo misalai domin kusanto da tunani ne kawai, misalin wannan a fili yake a kasashe, ta yadda an san ministoci sun san maras kyau, amma ba kowa ake zaba ba sai wanda aka san ba zai ci amana ba a bisa ilimin zahiri, sai dai wannan ba ya hana shi cin amana idan ya so ya ci.

Da shugaba ya san wadanda ba zasu ci amana ba a bisa badini da hakika to da su zai kawo a matsayin ministocinsa, sai dai ilimin mutane takaitacce ne, don haka sai su dogara da zahiri. Amma Allah mahaliccin kowa ya san wanda zai kiyaye har a badini, don haka ba ya zabar mutum sai wanda ya san yana da kiyayewa a zahirinsa da badininsa, sannan sai ya zabe shi a matsayinsa jakadansa, kuma ya ba shi baiwa da falala da ilimi maras iyaka.

Da wannan ne zamu ga cewa a fili yake babu wata isma da take hana zabi ga ma'asumi, kuma babu ismar da take kara zube ba tare da sanin tsarkin ruhin zababbun bayi ma'asumai ba. Don haka sun cancanci a girgiza musu, kuma a yaba musu, da wannan ne ma muka ga Allah madaukaki a cikin ayoyin Kur’ani mai girma yana girmama su girmamawa! Yana nuna kimar ayyukansu sakamakon dagewarsu kan biyayya gareshi dagewa!.

Hafiz Muhammad Sa'id

Sunday, September 13, 2009



back 1 2