Hadisin Manzila



 

 

Mene Ne Hadisin Manzila?

Ya zo a babin darajojin imam Ali (a.s) a littattafai masu yawa kamar Sahih Buhari da Sahih Muslim da Masnad Ahmad bn Hanbal, da Tirmizi, da Ibn Majah, cewa Manzon Allah (s.a.w) ya ce da Ali (a.s): “Kai a wajena kamar Haruna (a.s) ne da Musa (a.s), sai dai babu annabi bayana”. Sai ya tabbatar da duk wata alaka da take tsakanin Musa da Harun (a.s) amma domin gudun kada mutane su dauke Ali a matsayin Annabi sai manzo mai hikima ba tare da wata fasila ba sai ya togace annabta daga imam Ali (a.s).

Hadisin manzila "Hadisin Matsayi" Shi ne: Fadin manzon Allah (s.a.w) ga imam Ali (a.s) cewa: "Kai a wurina kamar matsayin Haruna wurin Musa ne, sai dai babu Annabi bayana". Sannan manzon rahama ya fadi wannan hadisi a wurare kamar haka:

1.    Ranar hada 'yan'uwantakar Juna tsakanin sahabbansa

2.    Ranar Badar

3.    Ranar Khaibar

4.    Ranar Tabuka

5.    Ranar Mubahala



1 2 3 next