Annabcin Annabi Musa (a.s)



Shin Annabcin Annabi Musa (A.S) Na Duk Duniya Ne Ko Kuwa?

Duba zuwa ga wannan maud’in yana bukatar bincike kan lamurra guda biyu; na farko: Kan da’awarsa zuwa ga tauhidi da kadaita Allah madaukaki. Na biyu: Kan batun shari’arsa da hukunce-hukuncen da ya zo da su daga ubangijinsa. Domin wadannan abubuwa ne guda biyu mabambanta; ta yiwu ya zo da kira ga tauhidi ga Banu Isra’il mutanensa kawai ko kuma ya kasance ya zo da kiran ga dukkan al’ummar duniya ne. Sannan yana iya yiwuwa ya zo da kiran tauhidi ga al’ummar kabilarsa kawai wato; Banu Isra’il, amma kuma ya kasance ya zo da shari’a ga dukkan mutanen duniya ne. Domin kasancewar kiransa zuwa ga tauhidi zuwa ga duniya ne gaba daya, ba ya tilasta kasancewar shari’arsa ta kasance ta duniya ce gaba daya, banda akasin hakan, wato; da shari’arsa ta kasance zuwa ga mutanen duniya ne gaba daya, to dole kiransa zuwa ga tauhidi na kadaita Allah ya kasance zuwa ga dukkan mutanen duniya ne. Don haka a nan muna da bincike guda biyu ke nan da zamu yi:

Na farko: Kiran Annabi Musa (a.s) zuwa ga kadaita Allah madaukaki;

Na biyu: Kasancewar shari’arsa ta game daukacin dukkan al’ummun duniya ne;

Wasu ayoyi masu yawa suna nuni da kasancewarsa an aiko shi ne zuwa ga Banu Isra’il, kamar ayar nan da take cewa: “Yayin da Musa yake cewa da mutanensa ya ku mutane….” Saffi: 5. Da ayar nan da take cewa: “Kuma hakika Musa ya zo muku da ayoyi (hujjoji) sannan sai kuka riki dan maraki…”. Bakara: 92. Da ayoyi masu yawa da suke nuni da aika Musa (a.s) zuwa ga mutanensa, sai dai wannan ba ya nuni a fili da cewa sakonsa bai shafi sauran al’umma ba, domin ga Annabi Shu’aibu (a.s) an aika shi zuwa ga mutanen “Madyana”, a lokaci guda kuma ga shi an aika shi zuwa ga mutanen garin “Aika”. Duba; surar A’arafi: 85, da kuma Shu’ara: 176-177.

Muna iya cewa da’awar Musa (a.s) ta kadaita Allah ta shafi Banu Isra’il da kibdawa ne, kuma muna iya fahimtar wannan daga surar nan ta A’arafi: 105, da 134, da surar Daha: 43, 44, 47, da surar Shu’ara: 16-17, 27, da surar Zukhuruf: 46, da surar Muzammil: 15-16, da surar Zariyat: 38. Da sauran ayoyin da suke nuna cewa an aika Musa zuwa ga Fir’auna da Banu Isra’il ne, kuma kiransa yana nuni da kawar da bautar gumaka, da tsafi, da sihirin Fir’auna da mutanensa, har ma aka yi kure tsakanin Annabi Musa (a.s) da masu sihiri kuma ya yi galaba a kansu. Wannan duk yana nuna mana yadda da’awarsa ta shafi wanin Banu Isra’ila na Kibdawa da makamantansu, sai dai duk da haka ba mu da wani dalili mai gamsarwa a kan cewa da’awarsa ta shafi duk duniya ne, kai har ma da Kibdawan.

Tana iya yiwuwa da’awarsa ta zo ne domin ta tseratar da Banu Isra’il, sai dai domin da’awarsa ta samu karbuwa to dole ne ya yi tattaunawa da fir’auna domin ya tabbatar masa cewa; daga Allah madaukaki yake, ta yadda za a ce; da tseratar da su zai yiwu ba tare da shan wannan wahalar ba, to da ya yi. Sannan muna ganin cewa; duk sa’adda ya tabbatar wa fir’auna cewa shi manzo ne daga ubangijinsa sai ya kara masa da cewa ka aika Banu Isra’il tare da ni. Daha: 47. Don haka ne ma zamu ga yayin da ya kasa tseratar da su ta hanyar tattaunawa da fir’auna sai ya dauki wata hanyar ta mu’ujiza domin ya tseratar da su. Ayoyin da suka zo kamar haka suna nuni da wannan: A’arafi: 134, Nazi’at: 17-19, Daha: 77, Yunus: 90, Dukhan: 24. Da kuma nuni da cewa; muhimmancin tattaunawa da fir’auna domin a samu tsiran Banu Isra’il ne. Hada da cewa wasu ayoyin sun nuna cewa bayan Nuhu (a.s) an aika annabawa (a.s) masu yawa zuwa ga mutanensu har zuwa kan Musa (a.s) zuwa ga fir’auna, kamar yadda muke iya gani a surar Yunus: 74-75.



1 2 next