Raddin Suka



Nasu Allah sun bayyana mana shi a littattafansu babu wani boye – boye, kuma idan ka kalli siffofinsa da yadda suke kwatantashi zaka ga yasha banban da Allah mai girma da daukaka, ga wasu yan misalai. Muhd Takiyyi (LA) ya fada a littasinsa Sahifatul Abraru Mujalladi na biyu shafi na 140 "Allah " na addinin Shi'a" yana ziyartar Husaini dan gidan Ali ya mika masa Hannu suyi musafaha ya zauna akan gadonsa". Tirkashi aiki ga mai kare ka kunji fa irin nasu Allan, haka Ziya'uddini Mahmud yace a littafinsa Kitabul Usulul Sitta Ashara shafi na 204 "Allah "na addinin shi'a" yana sauka a ranar Arfa a farkon zawali akan rakuminsa yana kewaya tsakanin mutane dama da hagu cinyoyinsa suna taba mutanan na Arfa" to duk wanda yayi imani da irin wadannan bayanan da suka gabata ba Musulmi bane, Kur'aninmu mus'hafi Usman da Hadisanmu da maganganun malamai da yawan gaske sun tabbatar da haka, kai du mutumin da hankalinsa yake garau ai yasan haka)).

Sai in ce maka: A nan ma ka ci kasa, kuma ka fadi warwas: ina ganin yana da kyau ka yi ilimi tukun sannan sai ka yi magana, ka daina magana kamar Aku da sai dai ya maimaita lafuzzan masu suka, bai san me suke nufi ba, Ka sani mawallafin wannan littafin abin da ya nakalto ya nakalto ne alhalin yana mai dogaro da abin ya karbo daga malamansa kuma ya rubuta, wannan kuwa yana nuna adalcinsa ga Sunnanci, ka sani Jaza'iri ya zamanto Shi'a ne daga baya, domin da farko ya kasance malami ne a sunnacin kafin ya karbi mazhabar Shi'a.

Koda yake wasu abubuwan da ka kawo suna nuna son rai ne, domin duk jahilci akwai sanin kage babu kyau, idan dai kana neman tsarki ga Allah to ka koma koyarwar Ahlul Baiti (a.s), ina ganin kana son nuna abin da ka yi imani da shi game da Allah ne sai kake neman dorawa kan Shi'a. Hakika kun kawo cewa Ahmad Bn Hambal yana gaisawa da Allah da hannu kamar yadda ya zo daga Manakibu Ahmad na Ibnul Jauzi.

Amma game da gaisawa da hannu da kuma rungumar juna da ubangijin talikai kun kawo cewa hakan zai yi da shi da Umar kamar yadda kuka karbo daga Ka'abu cewa farkon wanda zai yi rungume Ubangiji a ranar lahira shi ne Umar, kuma farkon wanda zai yi hannu da shi Umar. Almustadrak 3, shafi: 84. Ibn Majah 1, shafi: 39. da Kanzul Ummal, j 1, shafi: 578.

Hada da cewa mu ba ma kawar da ruwaya game da siffofin Allah madaukaki sai idan ta ci karo da Kur'ani da hankali, sannan kuma a mayar da ita ga muhkamar aya, kuma ta kasance babu tashbihi kuma babu ta'adili sai dai tanzihi.

Irin mahangarku game da Allah madaukaki da a koyarwarku da aka dauke shi da matsayin siffofi da ba su cancanci she ba, har kana da bakin magana kan masu tsarkake shi daga tashbihinku, kuna dauki Allah kamar haka:

Kamarsa da Annabi Adam (a.s) da tsayinsu irin daya (fatawa bn Baz, j 4, shafi: 226)

Kasancewarsa wani saurayi ne mai takalma biyu, mai gashi har baya, da korayen kafafu, yana da takalman silifa biyu na zinare, da wata ado ta zinare a fuska. (Ta'alikin Albani ga sunnar ibn Abi Asim No. 471)

Zaman Ubangiji kan al'arshi kuma yana da girma daidai al'arshin ne, sai dai al'arshin ya fi shi girma da kadan kamar girman 'yan yatsu hudu ne. (firdausil akhbar, j 1, shafi: 219). A littafin Akadul farid (j 6, shafi; 208) kuma macijiya ta kanannade al'arshin. Wannan kuwa yana nuna ta fi al'arshin tsawo sosai.

Zaman Allah kan kursiyyu: (tafsiru Dabari: j 3, s: 7)



back 1 2 3 next