Halayen Annabi-2



Halayen Manzon Allah (s.a.w) - 2

Idan kuwa zai ci abinci sai ya zauna kamar yadda bayi suke zama don kaskan da kai ga Allah (s.w.t), kuma ya zauna da nutsuwa sai ya ambaci Allah (s.w.t), sannan sai ya ci da 'yan yatsu uku ko hudu ko da tafinsa, kuma yana cin gabansa ne ba ya bin gaban wasu, sannan idan shi ne ya zo da abicin sai ya fara.

A kowane abu manzon Allah (s.a.w) yana kiyaye hakkin mutane, don haka ne ya kasance ba ya cin tafarnuwa ko albasa, ko wani abu da yake da warin da mutane suke cutuwa idan sun shake shi. Sai dai duk da haka ba ya kushe abin da ba ya cin sa, idan ya kayatar da shi sai ya ci, idan kuwa abin ci bai kayatar da shi ba sai ya bari ba tare da ya kushe shi ba.

Idan ya gama cin abinci sai ya sude hannunsa, sannan sai ya tsarkake ta da wani kyalle, sannan sai ya wanke hannun, ya shafe shi da wani kyalle, don haka ne ba a samun hannunsa yana kanshin abin da ya ci.

 Sannan ba ya ci shi kadai sai ya samo mai taya shi, yana ganin mafi sharrin mutane shi ne wanda ya ci shi kadai, ya daki bawansa, ya hana mutane abincinsa. Kuma ba ya cin mai zafi yana yana umarni da a bari sai ya yi sanya, yana ganin shedan yana da rabo a abinci mai zafi.

Sannan akwai abin ci masu yawa da ruwayoyi suka kawo cewa manzon Allah (s.a.w) yana cin su da suka hada da dabino, da sukari, da gishiri, da alkama, da duma, da kankana, da gishiri, da kayan marmari, da inabi, da gurasa, da nono tare da dabino. Haka nan yana cin nama gasasshe, yana ganin yana da amfnai wurin karfafa ji da gani, yana cin naman kaji, da tsuntsaye, yana son karfata daga tumaki da awaki. Kuma yana cin gurasa da mai, yana shan kunu, yana cin abubuwan da suke a kasa kamar irinsu dankali da makani.

Idan muka koma batun sha zamu ga yana sha a kwano, kuma yana sha bayan ya ambaci Allah sannan idan ya kare sai ya gode masa, yana zukar ruwa ne ba ya kwankwandarsa, kuma ba ya lumfashi a cikin kwanon shan ruwa, idan zai yi lumfashi sai ya yi nesa da kofi ko kwanon shan ruwan.

Sannan akwai matakai masu mihimmanci bayan ci kamar kurkure baki, da muka fi sani a  yau da yin burush kafin mutum ya kwanta domin kada abin da ya bari na kufan abinci ya lalata masa hakora, da sauran matakan tsafta da mai aminci ya yi nuni da su a aikace.

An ruwaito daga gareshi mai aminci cewa: Ka ci kana sha'awa, ka bari kana sha'awa. Wannan lamarin yana nuna mana muhimmancin rashin cika ciki ya yi yawa, don haka riko da wadannan nasihohi nasa mai aminci shi ne hanyar da zai samar da lafiya ga al'umma.

Akwa maganganun masu yawa a wannan babin da suka hada da abubuwan da  ya kamata a ci, da lokacin da ya kamata a ci, da zamanin da ya dace da cin su, da kuma abubuwan da bai kamata a ci ba, da amafanin abubuwan ci daban-daban, sai dai zmau takaita a nan zuwa wani jikon.

Amma idan muka duba adon manzon Allah (s.a.w) zamu ga ya ba wa wasu abubuwa muhimmanci kamar turare.  Imam Jafar Sadik (a.s) yana cewa: Manzon Allah (s.a.w) ya kasance yana kashe wa turare kudi fiye da yadda yake kashe wa abinci. Kuma ba a ba shi wani turare sai ya sanya shi yana cewa: Shi kanshinsa mai dadi ne, daukarsa mai sauki ce, kuma ya kasance yana yin turare da almiski. Kuma a cikin duhun dare ana iya gane shi da kanshin turarensa kafin a gan shi, don haka idan ya wuce sai a ce; wannan manzon Allah ne (s.a.w).

Ya kasance yana taje gashin kansa da gemunsa da matajin karfe ko na katako, kuma matansa suna taje masa gashinsa da gemunsa, sai su dauki gashin da ya fadi kasa, kuma sau da yawa yana taje gemunsa sau biyu a rana. Ya kasance yana son gyara gashi yana kin buja-buya, yana farawa da kai sannan sai gemu sai kuma sauran inda yake da gashi.

 Manzon Allah (s.a.w) ya kasance yana shafa mai, kuma yana farawa da girarsa sannan sai gashin baki, sai kansa sai gemu. Kuma yana sanya kwalli sau uku a dama sannan sai hagu sau biyu, kuma yana sanya kwalli har a lokacin azumi.

Ya kasance yana duba madubi, yana kuma duba ruwa ya gyara keyarsa, yana ado ga sahabbansa balle ga matansa. Yana cewa: Ubangiji yana son bawan da idan zai fita cikin mutanensa ya shirya musu ya yi musu ado.

Amma sunnonnin manzon Allah (s.a.w) a wannan lokacin musulmi sun yi wurgi da mafi yawancinsu, sai suka dauki wani abu daban ba su ba, aka jefar da mafi yawan dabi'unsa da halayensa, aka musanya su da wasunsu, sai musulmi suka musanya kaskan da kansa da girman kai da dagawa, kyawawan halayensa kuwa aka wurga su kwandon shara aka dauki munanan halaye aka yafa.

Manzon Allah (s.a.w) ya kasance yana kallon kasa-kasa yayin tafiya, yana fara wa wanda ya hadu da shi da sallama, ba ya magana sai gwargwadon bukata, yana girmama ni'imomin Allah ba ya rena komai daga garesu, sai ya gode wa Allah madaukaki, yana dariya amma ta murmushi, yana tambayar sahabbansa idan bai ga dayansu ba, yana tambayar mutane don ya san halinsu, yana tashi da zama bisa ambaton Allah, yana zama inda ya samu wuri ne, yana girmama abokan zamansa ba tare da ya nuna fifiko ba, ba ya hana wanda ya roke shi sai dai iban babu sai ya yi masa magana mai dadi ko addu'a ko ya yi masa nuni da inda zai samu bukatarsa, ba ya jayayya da nuna isa kan wasu don wulakanta su, ba ya hassada ko kullata, yana barin abin da babu ruwansa, ba ya yanke wa wani maganarsa, yana daidaita kowa a kallo, ya fi kowa fasaha, yana magana mai tattare da hikima, yana da yawan kunya, ya fi kowa karfi da jarumta, yana kuka don tsoron Allah, yana tuba da istigfari sau 70 a kowace rana, yana zama da talakawa, yana ci da miskinai, yana sadar da zumunci, yana dinke tufafinsa, yana gyara takalmansa, yana ci kamar yadda bayi suke ci, yana zama a kasa, yana hannu da talaka da mai kudi, ba ya wulakanta talaka don talaucinsa, yana sallama ga kowa talaka da mai kudi, babba da yaro, yana kallon mudubi, yana zabar mafi tsanani don saba wa ransa da saba wa son rai, yana cin gabansa, ba ya ci yana kishingide, yana sha da lumfashi uku, yana son yin abu da hannun dama; damansa domin abinci, hagunsa domin jikinsa, idan ya yi magana sai ya yi murmushi, mafi yawan zamansa yana kallon alkibla ne, idan aka zo da yaro sai ya yi masa addu'a ya kai shi dakinsa, kuma tayiwu yaron ya yi masa fitsari a daki sai ya bari sai mutanen sun tafi sai ya wanke da kansa, ba ya bari wani ya tafi tare da shi idan yana kan abin hawa sai dai idan mutumin zai hau tare da shi (wato manzon Allah ya goya shi kan dabba), idan kuwa mutumin ya ki hawa sai ya ce masa: Yi gaba sai ka same ni a wurin da kake so. Kuma ya kasance idan bai ga mutum kwana uku ba sai ya tabamya, idan ba ya nan ne sai ya yi masa addu'a, idan yana nan sai ya kai masa ziyara, idan maras lafiya ne sai ya je ya gai da shi.

Manzon Allah (s.a.w) ya kasance bai taba cewa da mai yi masa hidima don me ka yi kaza ba, sai dai ya ce; da ka yi kaza da ya fi. Yana kiran kowa da kinayarsa domin girmamawa, yana sanya kinaya ga maras kinaya, yana ba wa wanda ya shigo matashinsa, idan kuwa ya ki sai ya nace masa har sai ya karba, yana futowa bayan bullowar rana, domin yana yin addu'a ne tsakanin alfijir da bullowar rana, idan ya shiga gida sai ya zauna a farkon wurin da ya samu a kowa.

Ya kasance bai taba yi wa kowa magana gwargwadon hankalinsa ba, sai dai gwargwadon hankalin su mutanen domin tausaya musu, shi mai yawan rusunawa da roko ga Allah ne, mai yawan addu'a, yana yanke akaifarsa, yana rage gashin baki kafin ya fita sallar juma'a, yana yin raha don tausaya wa al'ummarsa domin kada wasu su wuce gona da iri a kansa su rike shi kamar yadda kirista suka riki Isa (a.s).

Yana yi wa na kusa da shi magana da abin da ya dace da su, idan suna maganar lahira sai ya yi tare da su, idan ta duniya ce sai ya yi tare da su, idan suka ci ko suka sha sai ya kasance tare da su. Ba ya duba na ha'inci zuwa ga abin da bai  halatta ba, ko nuni da hannu haka nan, idan ya yi magana sai ya maimaita sau uku domin mai ji ya fahimta kuma ya fahimce shi ko ya isa da shi ga mutanensa.

Hafiz Muhammad Sa'id

hfazah@yahoo.com