Nasabar Zahra



Fatima Azzahra ‘Yar Muhammad (A.S)

Sunanata da Nasabarta: Ita ce Fatima ‘yar Muhammad (A.S).

Babarta: KHadijatul Kubra (A.S).

Al-kunyarta: Uwar babanta, Uwar Raihantaini, Uwar Imamai.

Lakabinta: Zahra, Al-batul, Assidika, Al-mubaraka, Addahira, Azzakiyya, Al-mardiyya, Al-muhaddasa.

Tarihin haihuwarta: 20 Jimada Akhir a shekara ta biyar da aike gun Ahlul Baiti (A.S).

Inda aka haife ta: Makka Mai girma.

Mijinta: Imam Ali (A.S).

‘Ya’yanta: Imam Hasan (A.S) da Imam Husain (A.S), Zainab uwar musibu (Saboda musibar da ta gani a Karbala), Muhsin (wanda aka yi barinsa a jikin bango), Zainb karama (Zainab As-Sugura).

Tambarin zobinta: Aminal mutawakkilun.

Mai hidimarta: Fidda.

Tsawon shekarunta: 18 a mashhuriyar magana.

Tarihin sahahadarta: 3 Jimada Akhir shekara 11 hijira, a wata ruwaya Jimada Auwal, tana mai ciwon sukan nan… da barin jariri da karayar kirji da hudar nan ta kusa.

Inda aka binne ta: Madina. Amma ba wanda ya san inda kabarinta yake har yanzu.