Soyayyar Juna



Soyayyar Juna

Hujjatul Islam Muhammad Raishahari

Hafiz Muhammad Sa’id Kano

10 / 1

Soyayya Maras Kyau

Littafi:

“Ta yiwu ku ki wani abu sai ya kasance alheri ne gareku, kuma tayiwu ku so wani abu sai ya kasance sharri ne gareku, kuma Allah yana sani ku kuma ba ku sani ba” [1].

Hadisai:

240. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Kauracewa ita ce; ukubar soyayya[2].

241. Daga Imam Ali (A.S) ya ce: Saudayawa kauna ta dasu a lokaci guda[3].

242. Daga littafin shara’I’I, daga mufaddhal dan umar: na tambayi Abu Abdullahi Ja’afar dan Muhammad assadik (A.S) game da so, sai ya ce: zukata ne da suka bar ambaton Allah (S.W.T) sai Allah ya kwankwada musu azabar son waninsa[4].

10 / 2

Siffofin Mai Soyayya

Littafi:



1 2 3 next